AFIRKA
4 MINTI KARATU
Cutar Sankarau: Alamomi da hanyoyin magance ta
Cutar sankarau ta kashe akalla mutum 118 a Nijeriya tsakanin bara da bana sa'annan sama da mutum 1400 suka kamu da cutar.
Cutar Sankarau: Alamomi da hanyoyin magance ta
Hukumar CDC ta ce babbar hanyar samun kariya daga cutar ita ce yin rigakafi. Hoto/Getty images
23 Afrilu 2023

Cutar sankarau cuta ce da ke kashe jama’a da dama a fadin duniya.

Hukumar da ke yaki da cututtuka masu yaduwa ta Nijeriya NCDC ta bayyana cewa daga shekarar 2022 zuwa 2 ga watan Afrilun 2023, cutar ta sankarau ta kashe mutum 118 a jihohi 22 na kasar.

Haka kuma hukumar ta ce an samu mutum 1, 479 da suka kamu da cutar.

Hukumar da ke yaki da cututtuka masu yaduwa ta duniya CDC ta ce cutar tana barazana ga mutum miliyan 450 a kasashe 26 a nahiyar Afirka.

Mece ce sankarau?

Sanakarau wata cuta ce da ke kama mayafin da ke zagaye da kwakwalwa da lakka.

Akwai nau’o’in cutar sanakarau daban-daban, sai dai hukumar dakile cututtuka masu yaduwa ta Nijeriya ta bayyana cewa kwayoyin cutar da suka fi shahara wurin jawo sankarau sun hada da Neisseria da Haemophilus influenzae da kuma Streptococcus.

Haka kuma a cikin ukun nan sankarau din da aka fi kamuwa da ita, ita ce wadda kwayar cutar Neisseria ke jawowa.

Cutar ta sankarau dai ta fi kama kananan yara amma lokacin da ake annoba, tana kama har da manya.

Alamomin cutar sankarau

Hukumar NCDC ta bayyana cewa daga cikin alamomin cutar akwai ciwon kai da zazzabi da sankarewar wuya.

Haka kuma ta ce wanda ya kamu da cutar zai rinka gudun hasken fitila ko hasken rana haka kuma cutar tana kai ga har mutum ya suma.

Hukumar ta NCDC ta ce musamman ga yara kanana wadanda suka kamu da sankarau yana da wuya a ga wadannan alamomin, sai dai akasari yaran suna rashin walwala da kuma rashin cin abinci.

Haka kuma NCDC ta kara da cewa cutar dai tana iya sa mutum ya rinka amai da daukewar numfashi da kuma jinin mutum ya sauka.

Matakan kariya

Hukumar da ke yaki da cututtuka masu yaduwa ta duniya CDC ta bayyana cewa mataki mafi muhimmanci da mutum ya kamata ya soma dauka domin kiyaye kai daga kamuwa da sanakarau shi ne yin rigakafi.

Sauran matakan kariya daga cutar kamar yadda NCDC ta Nijeriya ta bayyana akwai kauce wa cunkoson jama’a sa’annan kuma a rinka tabbatarwa akwai isashen iska a cikin gida.

Hakan na nufin bude tagogi na da amfani domin samun isashen iska musamman da dare idan za a kwanta bacci.

Ganin cewa an fi samun sankarau a lokacin zafi, cunkusuwa a daki daya da babu isashen iska ma na taimakawa wurin kara yaduwar cutar.

Ga wasu daga cikin shawarwari da hukumar CDC ta bayar domin zama cikin koshin lafiya da kuma kare kai daga cututtuka irin sanakarau:

  • A rinka samun isashen hutu.

  • A daina matse wa marasa lafiya

  • Wanke hannu lokaci bayan lokaci da sabulu

  • A kuma rinka rufe baki da hanci da kyalle ko tolifefa idan za a yi tari ko kuma atishawa ( a rinka amfani da gwiwar hannu ko kuma gefen hannu idan babu kyalle).

MAJIYA:TRT Afrika da abokan hulda
Rumbun Labarai
Hatsarin mota ya yi ajalin fiye da mutum 1,000 a Nijar a shekarar 2023, fiye da 12,000 sun jikkata
Sabbin hotunan tauraron dan'adam sun gano alamun 'kaburburan bai-daya a El-Fasher a Sudan
MDD ta yi gargaɗin cewa yaƙin Sudan na gurgunta tattalin arzikin Sudan ta Kudu
Trump ya ce bai kamata Afirka ta Kudu ta kasance cikin G20 ba, ba zai je taronta a Johannesburg ba
'Yan Sudan sun ba da mummunan labarin yi wa mata fyade yayin da suke tserewa daga Al Fasher
An kashe mutane 40 a harin da aka kai wa taron jana'iza a yankin Kordofan na Sudan: MDD
Yadda biranen Afirka mafiya tsafta suke bayyana sauyin da ake samu a nahiyar
Sojojin Ruwa na Ghana sun kama ‘yan Nijeriya 10 da suka ɓuya a jirgin ruwan Panama a Tema
Harin jirgin sama maras matuƙi na RSF ya kashe mutane da dama a lardin Kordofan na Arewa a Sudan
Fiye da mutum 1,500 sun rasa matsugunansu a Sudan sakamakon taɓarɓarewar tsaro: MDD
Dakarun RSF sun kashe mata 300, sun yi wa 25 fyaɗe cikin awa 48 a Al Fasher – Minista
Amurka ta buƙaci a tattauna domin kawo ƙarshen yaƙin Sudan, ba amfani da ƙarfin soja ba
Ana fargabar dubban mutane na cikin 'mummunan hatsari' a birnin Al Fasher na Sudan da RSF ta ƙwace
Shugabar Tanzania Samia Hassan ta lashe zaɓen ƙasar da kashi 97.66 cikin 100
Tchiroma Bakary: Sojojin Kamaru sun yi wa jagoran 'yan adawar kasar rakiya zuwa wuri mai 'aminci'
Kudirin 1325 ya cika shekara 25: Me ya sa dole Afirka ta jagoranci samar da zaman lafiya a duniya
Dubban mutane sun tsere daga North Kordofan yayin da RSF ta zafafa kai hari a yankin Darfur na Sudan
Fararen-hula 177,000 sun maƙale a Al Fasher na Sudan, yayin da RSF ke ci gaba da kisa - Likitoci
Rundunar RSF ta amsa aikata 'take haƙƙi' a Al Fasher na Sudan
Kenya ta tabbatar da mutuwar mutum 11 'yan yawon bude ido a hatsarin jirgin da aka yi a kasar