Shugaban Turkiyya Recep Tayyip Erdogan ya ce taron koli na NATO da za a yi a Ankara a ranakun 7–8 Yuli zai zama "dandali mafi ƙarfi na musayar ƙwarewa".
Da yake jawabi a wajen liyafar cin abincin rana da aka shirya domin karrama shugabannin majalisun dokokin ƙasashen NATO a Istanbul ranar Litinin, Erdogan ya ce Ankara na musayar ƙwarewarta ta musamman da ƙawayenta a ƙungiyar NATO wajen tafiyar da rikice-rikicen yanki, tare da gogewa mai yawa da ta samu a cikin ƙawancen.
Ya ƙara da cewa Turkiyya na ƙara kashe kudade a fannin tsaro kuma tana cikin manyan masu ba da gudunmawa biyar na farko ga ayyuka da harkokin NATO, bisa ga alkawuran da aka ɗauka a taron Hague na 2025.
Erdogan ya ce kiyaye ƙarfin NATO na hana abokan gaba kai hari tare da ƙarfafa haɗin kai tsakanin ƙasashen ƙawancen ya zama mafi muhimmanci fiye da kowane lokaci a halin da ake ciki yanzu.
Ya yi kira da a samar da wata hanyar haɗin gwiwar tsaro da kariya ba tare da wani sharaɗi ba a faɗin ƙasashen NATO, wadda za ta shimfiɗa daga Texas zuwa Ankara.
Da yake magana kan yaƙin Rasha da Ukraine, Erdogan ya ce wajibi ne a samu sakamako a cikin lokaci mai zuwa domin kawo ƙarshen rikicin da ya fara tun shekarar 2022 ta hanyar tattaunawa.
Ya kuma bayyana cewa batun Falasdinu ne ke zama jigon rikice-rikicen Gabas ta Tsakiya, yana mai cewa ba za a samu zaman lafiya mai ɗorewa ba muddin Isra'ila ba ta daina ƙwace ƙasashen Falasdinawa ba.












