| Hausa
NIJERIYA
3 minti karatu
Shugabannin addinai a Nijeriya sun sa hannu kan yarjejeniyar inganta zaman lafiya da fahimtar juna
Fiye da shugabannin addinin Musulunci da Kiristanci 50 sun rattaba hannu kan wata yarjejeniyar zaman lafiya tsakanin addinai a Abuja, inda suka ƙaddamar da wata sabuwar ƙungiya da za ta yi aiki wajen inganta zaman lafiya da fahimtar juna.
Shugabannin addinai a Nijeriya sun sa hannu kan yarjejeniyar inganta zaman lafiya da fahimtar juna
Shugabannin Musulmi da na Kirista sun halarci taron a Abuja. Hoto / Muslim World League

Shugabannin addinin Musulunci da Kiristanci fiye da 50 sun rattaba hannu kan wata yarjejeniyar zaman lafiya tsakanin addinai a Abuja, inda suka ƙaddamar da wata sabuwar ƙungiya da za ta yi aiki wajen inganta zaman lafiya da fahimtar juna tsakanin mabiya addinai a faɗin Nijeriya.

Ƙididdiga ta nuna cewa akwai mutane miliyan 200 a Nijeriya, kuma al’ummar ƙasar ta kasu kusan daidai tsakanin arewa, inda Musulmi suka fi yawa, da kudancin ƙasar, inda Kiristoci suka fi yawa. Haka kuma akwai wasu al’ummomi da ke gudanar da addinan gargajiya.

A shekarar da ta gabata, gwamnatin Nijeriya ta musanta ikirarin Shugaban Amurka Donald Trump cewa Kiristanci na fuskantar wata “barazana mai girma ga wanzuwarsa” a ƙasar da ke Yammacin Afirka.

Masana sun sha yin watsi da ikirarin cewa ana gudanar da “kisan kiyashin Kiristoci” a Nijeriya, inda suka ce rikice-rikicen da ake fama da su a ƙasar sun kashe Musulmi da Kiristoci ba tare da nuna bambanci ba.

Ba a ambaci kalaman Trump ba a cikin sanarwar yarjejeniyar da aka rattaba wa hannu a hukumance ba a ranar Laraba a wani taro da Ƙungiyar Ƙasashen Musulmi ta Duniya (Muslim World League) ta shirya.

Muslim World League ƙungiya ce mai zaman kanta ta Musulunci da ke da hedikwata a Saudiyya.

‘Mun buɗe sabon shafi’

Sai dai gwamnatin Nijeriya da wasu ƙungiyoyi daban-daban sun ci gaba da ƙoƙarin nuna ci gaba wajen magance matsalar tsaro tun bayan kalaman Trump.

Babban Sakataren Muslim World League, Mohammad Al-Issa, ya ce akwai ƙwarin gwiwa daga mabiya addinan biyu wajen “buɗe sabon shafi.”

Ya ce, “Ba mu musanta cewa tsattsauran ra’ayi ya cutar da kowa ba; kowa ya fuskanci illar hakan.”

Shugabannin Kiristoci da Musulmi daga Nijeriya sun bayyana yarjejeniyar a matsayin wani sauyi mai muhimmanci.

John Praise Daniel, shugaban Northern Christian Religious Leaders' Assembly, ya ce yana fatan yarjejeniyar za ta taimaka wajen dakile kalaman da ke raba kan al’umma daga wasu malaman addini.

Ya ce, “Babu kalaman ƙiyayya, babu rashin girmama sauran ƙungiyoyin addini, kuma babu kiran mutane da kafirai.”

'Mu yi aiki tare'

Sakatare Janar na Jama’atu Nasril Islam, Khalid Abubakar, ya ce: “Ba kira ba ne na ka bar addininka, a’a, kira ne na haɗin kai da yin aiki tare cikin jituwa.”

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawan Nijeriya, Barau Jibrin, ya wakilci Shugaba Bola Tinubu a wajen bikin rattaba hannu kan yarjejeniyar. Gwamnonin jihohin arewacin Nijeriya uku ma sun halarci taron.

Jibrin ya ce a ranar farko ta taron na kwanaki biyu: “Gwamnati ta kuduri aniyar tabbatar da cewa mun kasance ƙasa guda mai haɗin kai, duk da bambance-bambancenmu, ko wane irin bambanci ne.”

Rumbun Labarai
Mutane 237 ne suka mutu sakamakon zazzaɓin Lassa a watanni bakwai na 2026 a Nijeriya - NCDC
Sojojin Nijeriya sun kashe Abu Khalid Al Muhajir da wasu  kwamandojin ISWAP tara a Borno
Masarautar Kano ta musanta bidiyon da ake yadawa kan Sarki Sanusi II ya samu 'carry-over' a jami'a
Super Falcons da Indomitable Lionesses na gogayyar shiga Gasar Kofin Duniya
Gwamnatin Nijeriya za ta fara sarrafa kayayyakin tsara iyali a cikin ƙasar
Hukumar EFCC ta rufe asusun gwamnatin Jihar Osun kwanaki kaɗan kafin zaɓen gwamna
Rundunar sojin Nijeriya ta sanya tukuicin N60m kan kwamandan ISWAP da mataimakinsa
An yi motsin ƙasa a wasu sassan Abuja
An saki gomman mutanen da aka yi garkuwa da su a Jihar Kwara bayan wata shida a hannun ‘yanta'adda
WAEC ta riƙe sakamakon jarrabawar ɗalibai 167,486
Dakarun Nijeriya sun kama mutanen da ake zargi da kai wa  'yan Boko Haram ƙwayoyi a Borno da Yobe
Gwamnati ta ba jami’o’i da kwalejojin Nijeriya umarnin korar ɗalibai da ke da alaka da satar mutane
'Yansandan Nijeriya sun kama mutum 48 a samamen da suka kai maɓoyar masu laifi a Zamfara
An saki alƙalin da aka yi garkuwa da shi a jihar Kebbin Nijeriya
Dakarun Nijeriya sun daƙile harin daren 'yanta'adda kan sansanin soji
'Yanbindiga sun kashe mutum 12, sun yi garkuwa da mata da yara a wani ƙauye Sokoto a Nijeriya
Nijeriya ta tura sojoji 86 domin aikin wanzar da zaman lafiya a Guinea-Bissau
Sojojin Nijeriya sun daƙile yunƙurin 'yanta'adda na garkuwa  da mutane 31 a Borno
Remi Tinubu ta nemi Saudiyya ta tallafa wa ilimin almajirai a Nijeriya
Nijeriya ta lalata makamai guda 2,819 da ta kama a matakin dakile rashin tsaro