Hukumar EFCC mai yaki da masu yi wa tattalin arzikin Nijeriya ta'annati ta ba da umarnin rufe wani asusun banki na Gwamnatin Jihar Osun da ke Kudu maso Yammacin Nijeriya, tana mai cewa ta gano nau’i na shige da fice na kuɗaɗen gwamnati da ake zargi, waɗanda ke da alaƙa da binciken da take yi kan zargin almundahanar kuɗi da ta kai kusan naira biliyan 11.
A wata sanarwa da ta wallafa a shafinta na X, EFCC ta ce ta fara wannan bincike ne tun a watan Maris na shekarar 2026, kuma ya shafi zargin karkatar da kuɗaɗen tallafi na kare muhalli da kuma na farfaɗo da na asusun rarraba kuɗaɗen gwamnatin tarayya wato FAAC.
“Da a ce ba a samu shige da ficen kuɗaɗen da ba a amince da su ba da ba tun daga 2 ga Agustan 2026, da ba a ɗauki wannan matakin ba na bincike da dakatar da hana shige da ficen kuɗaɗe,” in ji sanarwar ta EFCC.
" Hukumar ta lura da manyan kuɗaɗe da ake turawa zuwa asusun wasu kamfanoni daban-daban, lamarin da ya sa ta gaggauta rufe asusun domin dakatar da wannan yanayi."
Wannan mataki ya ƙara tsananta takaddamar da ke tsakanin hukumar yaƙi da cin hanci ta tarayya da Gwamnatin Jihar Osun, wadda ke zargin EFCC da wuce iyakokin ikon da doka ta ba ta, tare da yunƙurin tsoma baki a harkokin jihar gabanin zaɓen gwamna.
EFCC ta ce ta riga ta yi wa jami'ai da dama tambayoyi a matsayin wani ɓangare na binciken, ciki har da Akanta Janar na jihar.
Gwamnatin Osun ta yi watsi da matakin
Gwamnatin Jihar Osun ta yi kakkausar suka ga matakin, tana mai cewa haramtacce ne kuma yana da manufar siyasa.
Gwamna Ademola Adeleke ya ce rufe asusun gwamnatin zai kawo cikas ga gudanar da ayyukan gwamnati a lokacin zaɓe, yana kuma zargin cewa an ɗauki matakin ne domin raunana gwamnatinsa gabanin zaɓen gwamna.
Babban Lauyan Jihar kuma Kwamishinan Shari'a, Oluwole Jimi-Bada, shi ma ya kalubalanci halaccin matakin, yana mai cewa EFCC ba ta da iko a kundin tsarin mulki na rufe asusun gwamnatin jiha ba tare da bin hanyoyin doka da suka dace ba.
Sai dai EFCC ta yi watsi da zargin cewa lokacin ɗaukar matakin yana da alaƙa da siyasa, tana mai cewa abin da ta yi ya zama wajibi ne domin kare dukiyar jama'a.
Hukumar ta ce:
"A ko da yaushe Hukumar tana bayyana cewa ba ta nuna bangaranci ko bambancin addini, illa dai tana aiki ne domin kare muradun 'yan Nijeriya baki ɗaya."


















