Mambobin Kwamitin Tattaunawa na 4+4 na Libiya sun amince ranar Laraba kan wani tsarin ɗaukar sabon Shugaban Babbar Hukumar Zaɓe ta Ƙasar (HNEC) bayan ƙoƙarin aiwatar da tsarin da aka amince da shi a baya ya ci tura.
An cim ma matsayar ne a lokacin zama na bakwai na kwamitin a babban birnin Tunisiya, Tunis, in ji wata sanarwar da ofishin MDD a Libya (UNSMIL) ya fitar.
Kwamitin ya shafe watanni yana tattaunawa bayan wakiliyar MDD ta musamman Hanna Tetteh ta shaida wa Ƙwamitin Tsaro na MDD ranar 22 ga watan Afrilu cewa ta tattauna da kaɗan daga cikin masu ruwa da tsaki na Libya kan su bayyana hanyoyin aiwatar da matakai biyu na shirin MDD.
Shirin, wanda aka bayyana a ranar 21 ga watan Agustan shekarar 2025, an gina shi ne kan ginshiƙai uku: amincewa da wani tsarin zaɓe da zai samu karɓuwa ta fannin fasaha da siyasa yayin zaɓukan shugabana ƙasa da na 'yanmajalisa, da haɗa kan cibiyoyin ƙasa ta hanyar kafa gwamnatin haɗin gwiwa, da kuma ƙaddamar da tattaunawa ta ƙasa.
Daftarin yarjejeniyoyi
UNSMIL ta ce mahalarta zaman na ranar Laraba, wanda Tetteh ta jagoranta, sun cim ma matsaya kan tsarin naɗin shugaban hukumar zaɓe ta ƙasar.
“Sun kuma ci gaba da tuntuɓar juna bisa sauran tanade-tanaden daftarin yarjejeniyar na ƙarshe, inda dukkan ɓangarorin suka yarda su ci gaba da tattaunawa a mako mai zuwa a Tunis,” in ji sanarwar.
A lokacin zamansu na farko a birnin Rome ranar 29 ga watan Afrilu, mambobin kwamitin 4+4 sun yarda su sake fasalin hukumar zaɓen ƙasar da kuma ba da shawarar cewa Antoni Janar na ƙasar Al-Siddiq Al-Sour ya ba da sunan wani sabon shugaban hukumar daga cikin manyan alƙalai da suka yi fice da ƙwarewa da kuma rashin nuna bambanci.
Sai dai kuma, daga baya a yayin zamansa na shida a Tunis ranar 14 ga watan Yuli, kwamitin ya sanar da cewa an dakatar da ƙaddamar da waccan yarjejeniyar.
Yarjejeniyar ta baya bayan nan wani ɓangare ne na ƙoƙarin da MDD ke jagoranta na samar da wani yanayi na zaɓuka da zummar kawo ƙarshen rarrabuwar kan Libiya a siyasance.



















