| Hausa
GABAS TA TSAKIYA
2 minti karatu
Kakakin Majalisar Dokokin Iran ya buƙaci ’yan kasa su rage amfani da fetur
Kakakin Majalisar Dokokin Iran kuma babban mai shiga tattaunawar diflomasiyya, Mohammad Bagher Ghalibaf, ya ce wani ɓangare na yawan amfani da man fetur ya samo asali ne daga masana’antu, ba daga ’yan ƙasa kaɗai ba.
Kakakin Majalisar Dokokin Iran ya buƙaci ’yan kasa su rage amfani da fetur
Ghalibaf

Wani babban jami’in Iran ya yi kira ga ’yan ƙasar da su rage amfani da man fetur a ranar Talata, yayin da ƙasar ke fuskantar matsalar shigo da isasshen mai saboda takunkumin sojin ruwan Amurka.

Kakakin Majalisar Dokokin Iran kuma babban mai shiga tattaunawar diflomasiyya, Mohammad Bagher Ghalibaf, ya ce wani ɓangare na yawan amfani da man fetur ya samo asali ne daga masana’antu, ba daga ’yan ƙasa kaɗai ba.

Sai dai ya ce duk da haka, abin da ya fi muhimmanci shi ne rage yawan man da ake amfani da shi.

Washington ta kakaba takunkumin sojin ruwa ga tashoshin jiragen ruwan Iran ne bayan Tehran ta rufe Mashigar Hormuz, wata muhimmiyar hanyar jigilar mai da iskar gas daga yankin Gulf.

Amurka ta kuma sanar da wasu sabbin takunkumai masu yawa da nufin ƙara matsa wa tattalin arzikin Iran lamba.

A kwanakin baya, an ga dogayen layukan motoci a gidajen mai da ke Tehran.

Mataimakin Shugaban Iran, Mohammad Jafar Ghaempanah, ya ce a makon da ya gabata man fetur din da ake samarwa a cikin gida bai wadatar ba, kuma saboda takunkumin sojin ruwan Amurka, Iran ba ta iya shigo da isasshen mai daga waje.

A baya-bayan nan, Fadar Shugaban Ƙasar ta ce za a sake duba adadin man fetur da ake ware wa ’yan ƙasa.

Ghalibaf ya ce rage amfani da man fetur na buƙatar haɗin kan jama’a, yana mai cewa idan aka yi amfani da shi yadda ya kamata, Iran za ta iya dogaro da adadin man da take samarwa a cikin gida.

Ƙarin tallafin abinci

Yayin da hauhawar farashin kayayyaki da yaƙin ke ƙara tsananta matsin tattalin arziki ga ’yan Iran, Ghalibaf ya kuma sanar da shirin ƙara tallafin gwamnati.

Ya ce gwamnati da majalisa sun ƙuduri aniyar ƙara kuɗin da ake warewa shirin tallafin abinci na lantarki, musamman ga iyalan da matsin tattalin arziki ya fi shafa.

A watan Disamban da ya gabata, zanga-zangar nuna damuwa kan matsalar tattalin arziki ta rikide zuwa babbar zanga-zangar adawa da gwamnati, wadda ta kai kololuwa a watan Janairu kafin jami’an tsaro su dakile ta.

Ghalibaf ya jaddada cewa jin daɗin jama’a na daga cikin abubuwan da suka fi muhimmanci ga gwamnati.

Ya ce, a matsayinsu na jami’an gwamnati, ya kamata duk ƙoƙarinsu ya mayar da hankali wajen rage wa jama’a matsin rayuwa da kuma rashin gamsuwa, domin jin daɗin jama’a muhimmin ginshiƙi ne ga gwamnati.

Rumbun Labarai
Shugaban Siriya ya naɗa tsohon shugaban ƙungiyar SDF/YPG a matsayin mai ba shi shawara
Babbar ɗimuwar Netanyahu: Mafarkin Turkiyya na shirin kai hari
Shugaban Iran ya yi kira ga ƙasashen Musulmai su daina bari ana kai hare-hare daga cikin ƙasashensu
Hare-haren Iran sun ragargaza cibiyoyin leken asirin Amurka a Gabas ta Tsakiya: Rahoto
Iran ta yi gargaɗin cewa yaƙi da Amurka nan gaba zai iya shafar duka shiyyar da ma fannin makamashi
Trump ya ce an cire abubuwan fashewa daga Mashigar Hormuz, ya gargaɗi Iran kan dasa wasu
Saudiyya da Faransa sun goyi bayan kafa ƙasar Falasɗinu, sun buƙaci Isra’ila ta janye daga Lebanon
Hantarar da Amurka ke yi mana za ta ta'azzara ƙoƙarin diflomasiyya, in ji Iran
Iran ta ci gaba da nuna rashin tsoro yayin da Amurka ke ci gaba da ƙara mata matsin lamba
Ya kamata yaƙi da Amurka ya ƙare yayin da Tehran ke da  'iko da mutunci': Pezeshkian
Sabbin takunkuman da Amurka ta saka mana ta'addanci ne a fannin tattalin arziki, in ji Iran
Tsohon Ministan Tsaron Isra'ila Yaalon ya zargi Netanyahu da neman rikici da Turkiyya
Ko dabarun yaƙi na Iran za su sanya Amurka sake tunani?
Iran na duba yiwuwar kai hari kan cibiyoyin sojin Amurka da ke Turai: Rahoto
Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa ta dakatar da kasuwanci da Iran har 'sai abin da hali ya yi'
Saudiyya ta yaba wa sabon ƙawancen tsaron teku da ya fara aiki
Iran ta ce ta yi nasara a 'yaƙi da kuma diflomasiyya' bayan Trump ya nemi a yi saranda
Trump ya yi barazanar kai wa Oman harin bam idan ta 'kawo cikas' a tattaunawar Amurka da Iran
'Ba za a iya ƙwace Hormuz ta saƙon X ko jirgin dakon jiragen yaƙi ko jawabin zaɓe ba' — Iran
Amurka da Iran sun amince su tsawaita wa'adin yarjejeniyar tsagaita wuta, in ji majiyoyin Pakistan