| Hausa
AFIRKA
2 minti karatu
Fiye da mutum 5000 sun tsere saboda rashin tsaro da ke daɗa ƙamari a Darfur ta Yamma a Sudan: MDD
Da yawa daga cikin iyalan da lamarin ya shafa sun kasance waɗanda aka tilasta musu barin gidajensu ne kuma suka ƙetare zuwa cikin, in ji hukumar IOM ta Majalisar Dinkin Duniya.
Fiye da mutum 5000 sun tsere saboda rashin tsaro da ke daɗa ƙamari a Darfur ta Yamma a Sudan: MDD
Tsohon Hoto: Dubban mutane sun tsere daga ƙauyuka a yankin Sirba na West Darfur biyo bayan ɓarkewar yaƙi

An tilasta wa fiye da mutum 5,000 gudun hijira daga ƙauyuka 10 a jihar Darfur ta Yamma ta Sudan cikin ƙaruwar rashin tsaro da kuma arangama tsakanin sojoji da mayaƙan RSF, kamar yadda Hukumar da ke Kula da ‘Yancirani ta Majalisar Ɗinkin Duniya (IOM), ta bayyana.

Hukumar ta MDD, a wata sanarwar da ta fitar ranar Lahadi, ta ce tsarinta na bibiyar mutane ya yi kiyasin cewa mutum 5,135 sun tsere daga ƙauyukan Sirba na jihar Darfur ta Yamma zuwa ranar 8 ga watan Agusta biyo bayan ɓarkewar yaƙi a yankin Bir Saliba.

Da yawa daga cikin iyaen da lamarin ya shafa an tilasta musu barin muhallansu ne zuwa cikin Chadi, in ji hukumar.

A ranar Asabar, Gwamnan Darfur Minni Arko Minnawi ya ce sojin Sudan sun daƙile wani gagarumin harin da mayaƙan RSF suka ƙaddamar a kan Bir Saliba.

Muhimmin birni

Bir Saliba na arewa da El Geneina, baban birnin Darfur ta Yamma, kuma ana ganin wuri ne mai muhimmanci, saboda inda ya ke a kan hanyoyin da ke zuwa birnin. Yankin ya fuskanci yaƙi a-kai-a-kai tsakanin RSF da soji da dakarun da ke mara wa sojojin baya.

Yaƙi tsakanin sojin Sudan da RSF ya ci gaba tun ranar 15 ga watan Afrilu na shekarar 2023, biyo bayan rashin cim ma matsaya game da shigar da RSF ɗin cikin sojin ƙasar. Rikicin ya yi ajalin gomman dubban mutane tare da raba miliyoyin mutane da gidajensu.

Zuwa ƙarshen watan Yunin shekarar 2026, hukumar IOM ta tattara bayanan kimanin mutum miliyan 8.69 da aka raba da muhallansu a Sudan, tare da da mutum fiye da miliyan 4.64, waɗanda suka koma wasu yankuna a cikin ƙasar ko kuma suka ƙetara zuwa ƙasashe waje.

Rumbun Labarai
Kenya na binciken abin da ake tunanin guba ce wadda ta kashe giwaye 16
Guinea ta nemi Faransa ta mayar da ƙoƙon kawunan 'yan ƙasarta masu fafutuka
Ƙoƙarin kawar da sankarau: Manufar Afirka ta kawar da cutar baki ɗaya nan da 2030
Mutane fiye da 4,000 ne suka kamu da cutar Ebola a Jamhuriyar Dimokuradiyyar Kongo - Gwamnati
Kwamitin tattaunawa na Libiya ya cim ma matsaya kan tsarin ɗaukar shugaban hukumar zaɓe
Gargadin shugabannin Afirka kan cin abinci a makare da illolin shan siga da giya
Shugaba Biya na Kamaru ya yi sauye-sauye a shugabancin sojin ƙasar
Ghana ta amince da ɗaurin shekara 20 ga duk wanda ya mayar da gonar koko zuwa wani abu daban
Ɗaruruwan mutane sun yi hijira daga kudu maso yammacin Nijar saboda hare-haren 'yanta'adda
‘Yan Boko Haram sun kashe sojojin Nijar, in ji kafar watsa labaran gwamnati
Fitacciyar mawaƙiyar Afirka Ta Kudu ta soke kalankuwarta a Legas bayan an kori baƙi daga ƙasarta
Gwamnatin Ghana ta amince da shawara ƙara wa'adin mulkin shugaban ƙasa
Adadin 'yan ci-ranin da suka rasu ya kai 19 bayan dubbai sun tsallaka zuwa yankin Ceuta na Sifaniya
Biranen Afirka 25 da Amurka za ta rufe ayyukan bayar da biza daga ranar 1 ga Agustan 2026
Siyasar Kamaru: Ina Shugaba Paul Biya ya shiga?
Nijar ta dakatar da kamfanonin dillancin siminti 36 kan zargin ɓoye shi don haddasa ƙarancinsa
Hukumomin Libya a Benghazi sun kori baƙin-haure fiye da 117,000 daga ƙasar
Mutumin da ya fi kowa tsawo a Ghana Awuche ya rasu
Chadi ta sanar da shirin fita daga Kotun Hukunta Manyan Laifuka ta Duniya (ICC)
An gudanar da zanga-zanga a Tripoli saboda tsadar rayuwa da tabarbarewar ayyukan gwamnati