| Hausa
AFIRKA
2 minti karatu
Ɗaruruwan mutane sun yi hijira daga kudu maso yammacin Nijar saboda hare-haren 'yanta'adda
Wasu daga cikin mutanen da suka tsira sun tsere zuwa yankin Tahoua da ke kusa da iyakar Nijeriya, yayin da wasu ɗaruruwa suka nemi mafaka a Dogondoutchi, wani babban gari da ke da nisan kusan kilomita 100.
Ɗaruruwan mutane sun yi hijira daga kudu maso yammacin Nijar saboda hare-haren 'yanta'adda
Har yanzu hukumomi ba su fitar da adadin mutanen da suka mutu ko suka jikkata ba.

Ɗaruruwan mutane sun tsere daga gidajensu a kudu maso yammacin Nijar bayan jerin hare-haren da aka kai wa ƙauyukansu a tsakiyar watan Yuli, kamar yadda kafafen yaɗa labaran gwamnati da majiyoyin yankin suka bayyana.

Ba a taɓa samun adadi mai yawa na mutanen da suka yi gudun hijira a yankin na Dosso irin wannan lokaci ba, yankin da ke da iyaka da Nijeriya da Benin.

Yankin kan iyakar ya zama sabon wurin da hare-haren ta'addanci suka ƙaru tun shekarar 2025, bayan ƙungiyoyin da ke da alaƙa da al-Qaeda da kuma ƙungiyar Daesh sun fara kutsawa yankin, a cewar cibiyar sa ido kan rikice-rikice ta ACLED.

Wani jami'i a yankin ya shaida wa AFP cewa an tilasta wa mazauna ƙauyukan tserewa "a daidai lokacin noman damina" sakamakon "jerin hare-haren ta'addanci" da aka kai a tsakiyar watan Yuli.

Masu AlakaTRT Afrika - ‘Yan Boko Haram sun kashe sojojin Nijar, in ji kafar watsa labaran gwamnati

Wasu daga cikin waɗanda suka tsira sun tsere zuwa yankin Tahoua da ke kusa da iyakar Nijeriya, yayin da wasu ɗaruruwa suka nemi mafaka a Dogondoutchi, wani babban gari da ke da nisan kusan kilomita 100 (mil 60), kamar yadda gidan talbijin na gwamnati ya ruwaito.

"Wadannan hare-hare na farko sun faru ne aƙalla a ƙauyuka uku a ranar 17 ga Yuli, inda suka yi sanadin mutuwa da jikkatar mutane da dama, dukkansu fararen-hula," kamar yadda wata majiya daga yankin ta shaida wa AFP.

Har yanzu hukumomi ba su fitar da adadin mutanen da suka mutu ko suka jikkata ba.

A ranar Juma'a, gwamnan yankin Dosso, Kanal Bana Alhassane, ya bayyana a gidan talabijin na gwamnati cewa za a ƙara tsaurara matakan tsaro domin bai wa mazauna damar komawa gidajensu da ci gaba da noma.

A cewar Majalisar Ɗinkin Duniya, Nijar na da fiye da mutane 450,000 da suka rasa matsugunansu a cikin ƙasar sakamakon hare-haren ta'addanci.