Wani jami’in Hizbullah ya shaida wa AP cewa, ‘yan kungiyar sun samu raunuka a sassa daban-daban na kasar Labanon da Syria / Hoto: AFP

Akalla mutum tara ne suka mutu sannan wasu sama da 2,750 da suka hada da mayakan Hizbullah da likitoci, suka jikkata, a lokacin da na’urorinsu na yada labarai suka fashe a fadin kasar Lebanon, kamar yadda kafafen yada labarai da jami’an tsaro suka bayyana.

Wani jami’in kungiyar Hizbullah da ya nemi a sakaya sunansa ya shaida wa kamfanin dillancin labarai na Associated Press cewa, ‘yan kungiyar sun samu raunuka a sassa daban-daban na kasar Labanon da Syria, a lokacin da wasu na'urorinsu na hannu suka fashe a ranar Talata.

Jami'in ya zargi Isra'ila da tayar da na'urorin, inda ya kara da cewa, wannan shi ne "tabarbarewar tsaro mafi girma" da kungiyar ta fuskanta a yakin kusan shekara guda da Tel Aviv.

Wasu majiyoyin tsaro biyu sun shaida wa kamfanin dilancin labaran Reuters cewa mayakan Hizbullah biyu da suka hada da dan majalisar dokokin Hizbullah ne suka mutu sakamakon fashe-fashen.

Bugu da ƙari, an kuma kashe wata karamar yarinya a yankin Baalbek da ke arewa maso gabashin kasar Lebanon, a cewar kafofin yada labaran Lebanon.

Rahotannin sun bayyana sunanta da Fatima Jaafar Abdullah 'yar shekara 9 'yar wani dan Hizbullah.

Kazalika, jakadan Iran a birnin Beirut ya samu rauni sakamakon fashewar wani abu amma raunin da ya samu bai yi tsanani ba, kamar yadda kafafen yada labaran kasar suka ruwaito.

"Jakadan Iran a Lebanon Mojtaba Amani ya samu rauni sakamakon fashewar wani abu," in ji gidan talabijin na kasar, ya kara da cewa "yana cikin hayyacinsa kuma ba ya cikin wani hadari."

A nata bangaren ma'aikatar lafiya ta kasar Lebanon ta bukaci dukkan 'yan kasar da suka mallaki na'urorin sadarwa na pager da su yi gaggawar kawar da su.

Wannan lamari dai shi ne irinsa na farko tun bayan da Isra'ila da kungiyar Hizbullah suka fara musayar wuta a kullum bayan da Tel Aviv ta kaddamar da yakin Gaza a watan Oktoban bara.

'Sabbin yayi'

'Yan jarida da masu daukar hoto a kudancin birnin Beirut sun ga motocin daukar marasa lafiya suna garzayawa da wadanda suka jikkata zuwa asibitocin yankin.

Kungiyar agaji ta Red Cross ta kasar Lebanon ta ce karin motocin daukar marasa lafiya 50 da kwararrun likitocin gaggawa 300 na cikin shirin ko-ta-kwana domin kai daukin wadanda lamarin ya rutsa da su sakamakon fashewar bututun mai.

Wakilin Kamfanin Dillancin Labaran Faransa na AFP a Gabashin Labanon ya ce an jikkata wasu da dama a irin wannan lamari a yankin kwarin Bekaa na kungiyar.

Kamfanin dillancin labarai na kasar Labanon ya ba da rahoton "wani lamari na tsaro da ba a taba ganin irinsa ba" game da "na'urorin hannu" sun tashi a yankuna da dama.

Kamfanin dillancin labaran Reuters ya rawaito jami'an tsaro cewa wadannan na'urori na pagers da suka tarwatse na daga cikin irin na baya-bayan nan da kungiyar Hizbullah ta samu a watannin baya.

Kungiyar Hizbullah ta bukaci mambobinta da su guji amfani da wayoyin hannu bayan yakin da Isra'ila ke yi a Gaza ya fara kauce wa keta fasaha.

'Yan Hizbullah suna sadarwa ta hanyar tsarin sadarwarsu.

TRT World