Ndop shi ne gari mafi yawan jama'a a lardin Ngoketundjia da ke Arewa Maso Yammacin Kamaru./Hoto: Getty Images

Rahotanni daga Kamaru na cewa 'yan a-waren kasar sun sace ma'aikatan gine-gine da dama a wurin da ake gina dakin binciken kimiyya a Arewa maso Yammacin kasar.

Kamfanin dillancin labaran Cameroon News Agency ya rawaito cewa an sace ma'aikatan ne a makarantar Government Bilingual High School (GBHS) a garin Ndop.

Ndop shi ne gari mafi yawan jama'a a lardin Ngoketundjia da ke Arewa Maso Yammacin Kamaru.

Rahotanni sun ce satar mutanen, wadanda ya zuwa yanzu ba a san adadinsu ba, ta sa aiki ya tsaya cak a wurin.

Majalisar dokokin yankin Arewa maso Yammacin kasar ce ta dauki nauyin gina dakin binciken kimiyya na makarantar GBHS.

An yi garkuwa da ma'aikatan ne a ranar da gwamnan Arewa maso Yammacin kasar ya gargadi 'yan a-waren, sannan ya bukace su ajiye makamansu.

Rikici ya fara ne tsakanin yankin Arewa maso Yamma da kuma Kudu maso Yamma a shekarar 2016, inda malaman makaranta da lauyoyi suka kalubalanci kakaba musu magana da tsarin Faransanci.

A tsawon shekara shida na rikicin, fiye da mutum 6,000 ne suka rasa rayukansu yayin da wasu 600,000 suka kauracewa muhallinsu, a cewar bayanai.

TRT Afrika