Tsohon shugaban Hukumar Ƙwallon Kafa ta Afirka CAF, Issa Hayatou ya rasu

Tsohon shugaban Hukumar Ƙwallon Kafa ta Afirka CAF, Issa Hayatou ya rasu

Tsohon shugaban hukumar ƙwallon ƙafa ta Afirka, CAF Issa Hayatou ya rasu yana da shekaru 77.
Dan Kamarun ya kasance shugaban hukumar kwallon kafa ta Afirka (CAF) na tsawon shekaru 29. / Hoto: Reuters

Tashar talabijin ta Kamaru ta ce tsohon shugaban hukumar kwallon kafar Afirka Issa Hayatou ya rasu a ranar Alhamis kwana daya da cikarsa shekaru 78 a duniya, bayan ya sha fama da rashin lafiya.

Dan Kamarun ya kasance shugaban hukumar kwallon kafa ta Afirka (CAF) na tsawon shekaru 29 daga 1988 har zuwa lokacin da aka hambarar da shi a wani lamari mai ban mamaki a shekarar 2017.

Ya kuma rike mukamin shugaban hukuma ta FIFA na riƙo daga 2015-2016 bayan da hukumar kwallon kafa ta duniya ta dakatar da Sepp Blatter.

Hayatou, wanda ɗan'uwansa ne firaministan kasar Kamaru, ya kasance mai kula da harkokin wasanni a tsawon rayuwarsa.

Zargin cin hanci

Ya kasance mamba na kwamitin Olympics na kasa da kasa daga 2001-2016, bayan haka ya zama mamba na girmamawa.

A shekarar 2011 hukumar ta IOC ta ladabtar da Hayatou kan rawar da ya taka a badakalar karbar cin hanci a hukumar ta FIFA.

An tsawatar masa bayan da shirin BBC Panorama ya yi ikirarin cewa ya karbi kusan dala 20,000 daga rusasshen kamfanin tallan wasanni na ISL a shekarar 1995.

Hayatou ya musanta cin hanci da rashawa kuma ya ce kudaden kyauta ne ga kungiyarsa.

Fafutuka

Zamansa na shugabancin kwallon kafar Afirka ya sa wasan ya samu ci gaba duk da cewa ana zargin Hayatou da jan kafa wajen kawo sabbin sauye-sauye.

Hayatou ya kalubalanci Blatter a matsayin shugaban FIFA a shekarar 2002, amma ya sha kaye yayin da kasashen Afirka da dama suka yi watsi da shi a kuri'ar adawa da Swiss.

Reuters