| Hausa
KASUWANCI
1 minti karatu
Trump ya ce Amurka za ta karɓi gangar ɗanyen mai miliyan 50 daga Venezuela
Donald Trump ya ce za su karbi ganga miliyan 30 zuwa 50 na danyen mai daga Venezuela a karkashin sabuwar yarjejeniyar da aka kulla.
Trump ya ce Amurka za ta karɓi gangar ɗanyen mai miliyan 50 daga Venezuela
Shugaban na Amurka ya ce za a sayar da man a kasuwar Amurka kuma shi zai kula da kudin don amfanin Amurka da Venezuela. / TRT World and Agencies

Shugaban Amurka Donald Trump ya ce Amurka za ta karɓi ganga miliyan 30 zuwa 50 na man fetur daga Venezuela da aka sanya wa takunkumi, don a sayar da shi a farashin kasuwa.

Trump ya bayyana cewa hukumomin riƙon ƙwarya na Venezuela za su miƙa man fetur ɗin kuma shi da kansa zai kula da yadda za a gudanar da kuɗaɗen da aka sayar da shi.

"Hukumomin riƙon ƙwarya a Venezuela za su bayar da ganga miliyan 30 zuwa 50 na man fetur da aka sanya wa takunkumi ga Washington," in ji Trump.

Masu AlakaTRT Afrika - Amurka ba za ta bari kowa ya ci gaba daga inda Maduro ya tsaya ba - Trump

"Man da muka samu daga Venezuela za a sayar da shi a farashin kasuwa, kuma ni ne zan kula da yadda za a gudanar da kuɗaɗen da za a samu daga sauar da shi," in ji shugaba Trump.

Trump ya ce ya umarci sakataren makamashi na Amurka da ya aiwatar da shirin nan-take.

"Na umarci sakataren makamashi da ya aiwatar da shirin nan-take," in ji shi, ya ƙara da cewa za a yi jigilar man ta amfani da tankunan ajiya sannan a aika shi zuwa tashoshin fitar da man fetur na Amurka.

Rumbun Labarai
Shigar kuɗaɗe daga waje cikin Nijeriya don zuba jari ta ƙaru da kusan kashi 90% a 2025 – Hukumomi
Hauhawar farashin mai ta janyo aiki daga gida da karatu daga nesa a wasu ƙasashen Asiya
Harin da aka kai wa 'yan kasuwar Ghana a Burkina Faso ya sa farashin tumatur ya tashi
Naɗin 'ya'yan Dangote mata uku a manyan muƙamai: Sabon babi a tsarin gado na kasuwancin iyali
China za ta soke karɓar harajin fitar da kayayyaki daga ƙasashen Afirka 53
Me ya sa farashin zinare ke tashi a lokacin rikicin siyasa a duniya?
Gwamnatocin Afirka sun juya ga tsarin Bankin Musulunci bayan nasarar Sukuk a Benin
Ana sa ran kasuwanci tsakanin Turkiyya da Nijeriya ya kai dala biliyan 10 saboda sabbin yarjeniyoyi
Afrika na amfani da tagomashin da zinari yake samu don ƙara ƙarfin arziƙinta
Ghana ta biya basussukan dala biliyan 1.47 na fannin makashi da ake bin ta
Kamfanin Dangote ya yi watsi da ikirarin rufe matatar mansa
Me ya sa hanyoyin teku da aka toshe ke tayar da kura a Gabashin Afirka?
ECOWAS za ta cire harajin tafiye-tafiyen jiragen sama tsakanin ƙasashen Yammacin Afrika a 2026
Manyan ƙere-ƙeren fasaha na Afirka da suka yi tasiri a duniya
Abu biyar da ya kamata ku sani kan Taron G20 na farko a Afirka
An cire Nijeriya daga jerin kasashen da ake sa wa ido kan safarar kudade ba bisa ka'ida ba a duniya
Bai kamata kasuwanci da Afirka ya zama buƙatar ɗiban ma’adanai ba: Ministan Nijeriya Tuggar
Jamhuriyar Nijar ta kafa cibiyar tsaron intanet
Kamfanin simintin Dangote ya fara aiki a ƙasar Ivory Coast
Ana hasashen mambobin OPEC+ za su ƙara yawan fetur ɗin da suke fitarwa yayin da farashinsa ke karewa