| Hausa
NIJERIYA
3 minti karatu
An yi jana'izar manoma 26 da aka kashe a harin 'yanbindiga a Jihar Zamfara a Nijeriya
Hukumomin yankin sun ce an kai wa manoman harin ne yayin da suke aiki a gonakinsu a Ƙaramar Hukumar Kaura Namoda ta Jihar Zamfara a ranar Alhamis.
An yi jana'izar manoma 26 da aka kashe a harin 'yanbindiga a Jihar Zamfara a Nijeriya
An yi jana'izar manoma 26 da aka kashe a harin 'yanbindiga a Jihar Zamfara a Nijeriya

An yi jana'izar manoma 26 da aka kashe a wani harin 'yanbindiga a Jihar Zamfara da ke arewa maso yammacin Najeriya a ranar Juma'a, kamar yadda majiyoyin yankin da wata sanarwa ta hukumomi suka tabbatar.

Hukumomin yankin sun ce an kai wa manoman harin ne yayin da suke aiki a gonakinsu a Ƙaramar Hukumar Kaura Namoda ta Jihar Zamfara a ranar Alhamis.

Kisan ya sake tayar da fargaba a tsakanin al'ummomin manoma, inda da dama daga cikinsu suka daina zuwa gonakinsu sakamakon hare-haren da ƙungiyoyin 'yanbindiga masu ɗauke da manyan makamai ke ci gaba da kai wa a yankin arewa maso yammacin ƙasar.

Yayin wata ziyarar jaje da ya kai wa al'ummar da abin ya shafa a madadin Gwamna Dauda Lawal Dare, Mataimakin Gwamnan Zamfara, Mani Malam Mummuni, ya buƙaci mazauna yankin su ƙara haƙuri, yana mai cewa gwamnatin jihar na ci gaba da jajircewa wajen kawo ƙarshen ayyukan ƙungiyoyin masu ɗauke da makamai.

"Gwamna ya aiko ni in ce ku ƙara haƙuri. Ba ku kaɗai abin ya shafa ba. Yana sane da halin da mutanen Zamfara gaba ɗaya ke ciki," in ji Mummuni.

Ya kuma bayyana cewa gwamnatin jihar ba za ta shiga tattaunawa da ƙungiyoyin masu ɗauke da makaman ba.

"Da yardar Allah za mu magance su, amma ba za a yi wata tattaunawa da su ba, domin yaudara ce, ƙarya ce, kuma ta'addanci ne," in ji shi.

Sabbin kashe-kashen sun zo ne a daidai lokacin da hare-haren 'yan bindiga ke ci gaba da addabar al'ummomin manoma, manyan tituna da ƙauyuka a yankunan arewa maso yamma da arewa ta tsakiya ta Nijeriya.

Hare-haren sun haɗa da kashe-kashe, garkuwa da mutane, satar shanu da kuma karɓar kuɗin fansa.

Wannan hari ya biyo bayan wasu munanan hare-hare da aka kai a cikin makonnin baya.

A watan Yuni, aƙalla manoma 17 aka kashe, yayin da wasu 13 suka jikkata lokacin da ake kai musu hari a gonakinsu da ke Goron Namaye, a Ƙaramar Hukumar Maradun ta Jihar Zamfara.

Harin ya faru ne kwanaki kaɗan bayan da 'yan bindiga suka sace mazauna yankin 39 da suka taru domin tattaunawa kan yadda za a sako 'yan uwansu da aka yi garkuwa da su.

Tun da farko a watan, wani hari da aka kai a ƙauyen Gora, shi ma a Ƙaramar Hukumar Maradun, ya yi sanadin mutuwar manoma shida, jikkatar kusan mutum 10, tare da yin garkuwa da wasu mazauna yankin.

Rikicin ya wuce Zamfara kaɗai, domin a cikin 'yan watannin nan ƙungiyoyin masu ɗauke da makamai sun kai hare-hare masu muni tare da yin garkuwa da mutane da yawa a jihohin Katsina, Kaduna, Neja da Sokoto.

Haka kuma hare-haren na ƙara yaɗuwa zuwa wasu sassan arewa ta tsakiya da kudu maso yammacin Najeriya.

A farkon wannan watan, rundunar sojin Nijeriya ta sanar cewa dakarunta tare da haɗin gwiwar masu aikin sa-kai sun kashe fiye da mutum 300 da ake zargin 'yan bindiga ne a wani babban farmaki da suka kai a Jihar Zamfara.

Rundunar ta bayyana farmakin a matsayin ɗaya daga cikin manyan hare-harenta na baya-bayan nan kan ƙungiyoyin masu ɗauke da makamai a yankin.

Sai dai duk da nasarorin da sojoji ke samu a wasu hare-hare, ƙungiyoyin masu ɗauke da makaman na ci gaba da sake haɗa ƙarfi a cikin dazuka masu nisa, inda suke samun kuɗaɗen gudanar da ayyukansu ta hanyar kuɗin fansa, haƙar ma'adinai ba bisa ƙa'ida ba da kuma satar shanu.