Shugabanni na neman mafita kan rikicin da ya addabi jihar Benue ta Nijeriya
NIJERIYA
5 minti karatu
Shugabanni na neman mafita kan rikicin da ya addabi jihar Benue ta NijeriyaRikici tsakanin al’ummomi da na ‘yan bindiga a jihar Benue da ke arewa ta tsakiyar Nijeriya ya kazance, inda a kwanakin aka kashe mutane da dama tare da lalata matsugunai a yankunan daban-daban na jihar.
/ AP

Kalaman da shugaban Nijeriya Bola Tinubu ya yi a jihar Benue mai cewa “ran dan-adam ya fi na saniya daraja” sun dauki hankalin ‘yan kasar, sakamakon yadda hakan ke nuna kamarin da rikici tsakanin makiyaya da manoma ya yi a wasu yankunan Nijeriya.

A daren Asabar 14 ga Yuni ne aka samu wani mummunan farmakin ‘yan bidinga a wasu garuruwan jihar Benue da ke arewa ta tsakiyar Nijeriya. Kashe-kashen na baya-bayan nan sun auku ne a garuruwan Yelwata da Daudu da ke karamar hukumar Guma ta jihar.

Mabambantan rahotannin sun nuna cewa an rasa rayuka da suka kai 100, baya ga tarin wadanda aka raunata, da kuma gidajen da aka banka wa wuta. Sauran yankunan da rikicin kan shafa a jihar Benue sun hada da Naka, Apa, da Agatu.

Tun wayewar gari ranar Lahadi ne, wasu matasa suka shiga zanga-zanga kan neman a dauki mataki. An ga dandazon mutane a titunan Makurdi masu dauke da allunan da ke neman gwamnatin tarayya ta shiga lamarin da gaske don kare al’umma.

An samu karuwar zaman dar-dar a jihar ta Benue a shekarun nan, amma a baya-bayan nan rikicin tsakanin makiyaya da manoma da kuma tsakanin kungiyoyin dake dauke da makamai. Sannan akwai rikici tsakanin kabilar Tiv da Jukun akan iyaka da Taraba.

Shugaban darikar katolika ta duniya, Fafaroma Leo ya yi allah-wadai da rikicin, sannan ya yi addu’a ga rayukan da suka salwanta a Benue, yayin hudubarsa ta ranar Lahadi, inda ya ce abin ya shafi masu gudun hijira da ke neman mafaka a sansanin cocin Katolika na garin Yelwata.

Ita ma kungiyar makiyaya a Nijeriya ta Miyatti Allah, wato MACBAN ta yi tir da hare-haren da ke faruwa a Benue. Sai dai kungiyar ta nemi a guji dora alhakin rikicin kan Fulani makiyaya, da kuma munana wa kabilarsu zato.

 

Ziyarar Tinubu

Ranar Laraba kwana hudu da harin, shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu ya kai ziyarar jaje jihar ta Benue, inda ya duba masu raunuka da ke jinya a asibitin koyarwa na Jami’ar Jihar Benue Makurdi

Yayin ziyarar tasa, Tinubu ya nemu Babban Hafsan sojin kasar, janar Christopher Musa da kuma dakarun kasar da su nemo maharan don a musu shari’a.

Ya kuma ba da umarnin gudanar da sulhu tsakanin bangarorin da ke artabu da juna, inda ya nemi gwamnan jihar Benue, Hyacinth Alia da ya kira taron tattaunawa da kafa kwamitin warware sabani da sasantawa don kawo karshen zubar da jini.

Shugaba Tinubu ya yi rokon zaman lafiya a jihar, kuma ya ja kunnen shugabannin al’umma da na siyasa su bar kalaman tunzuri,.

Sai dai da yake jawabi ga shugaba Tinubu, sarkin kabilar Tiv, Tor Tiv ya fada wa shugaba Tinubu cewa, harin ya wuce na jayayya, na “kisan kiyashi ne”.

Shi ma wani mai nazari da sharhi kan rikice-rikice a Nijeriya, malam Isa Sanusi, ya yi gargadin cewa ya kamata a yi bincike kafin a dora alhakin su waye suke kai hare-haren. Ya ce tabbas akwai rikici tsakanin makiyaya da manoma, amma yanzu abin ya wuce haka.

 

Matakan kai dauki

Wasu rahotannin sun ce shugaba Tinubu ya amince da kafa rigar shanu ta zamani a jihar ta Benue, don kawo karshen takun-saka tsakanin makiyaya da manoma, yana mai cewa Nijeriya na da isasshiyar kasar  da za ta wadaci kowa da kowa, ba tare da an samu fadace-fadace ba.

Ita ma rundunar sojin Nijeriya ta sanar da fara amfani da jiragen sama don yin sintiri a samaniyar babban brnin jihar Benue, Makurdi da sauran sassan jihar.

Sannan a bangaren ‘yan sanda kasar, Babban Sufeton ‘Yan Sanda na kasa, Mr Kayode Egbetokun ya sanar da karbe ragamar kula da tsaro a jihar tare da tura runduna ta musamman don dakile rikicin.

 

Rashin hukuntawa

Sai dai sau da yawa, hukumomi da masu saka ido sukan dora alhakin hare-haren kan ‘yan bindiga da ba a san ko su waye ba. Sannan daga bisani ba za a ji labarin an hukunta wadanda aka zarga ba ko aka samu da laifi ba.

Wannan ya sa wasu masana da masharhanta kan tsaro a Nijeriya suna nuna damuwa kan rashin bin kadin wadanda aka zalunta. Har ta kai wasu na ganin dacewar gwamnati ta kafa dokar ta baci a yankunan da abin ya yi kamari.

Mal Isa Sanusi ya ce dole sai mahukunta da jami’an gwamnati sun fuskanci matsalar da gaske domin tabbatar da duk wadanda suke da hannu an hukuntasu, bisa doka. Ya ce “Ya kamata a saka sabbin dabarun kare kauyuka da inganta tsaro a karkara. Sannan a fuskanci matsalolin talauci da rashin adalci tsakanin al’umma”.

Da take yin tir da kashe-kashe a jihar Benue, Kungiyar Kiristoci ta Nijeriya, CAN ta yi kira ga gwamnati ta dauki matakin gaggawa don dakile matsalar tsaro a yankunan kasar.

A wata sanarwar manema labarai da shugaban CAN, Archbishop Daniel Okoh ya sanya wa hannu, kungiyar ta jajanta wa dangin wadanda abin ya shafa, inda ta ce hare-haren suna kassara iyalai da ta’azzara matsalar tsaro a kasa.

CAN ta kuma nemi gwamnati ta aike da dakarun da za su karfafi jami’an tsaro a yankin, domin kare al’umma da garuruwan da ke fama da rikicin, da maido da zaman lafiya mai dorewa.

Sa’annan ta yi da a yi bincike kan kashe-kashen, kuma sun jaddada bukatar yin adalci domin rusa kaurin sunan da masu aikata manyan laifuka suka yi, na kubuta daga hukuncin doka, wanda ke sanyawa suna ci gaba da cin karensu ba babbaka.

Rumbun Labarai
NDLEA ta kama hodar iblis da aka ɓoye cikin kwanon abinci a filin jirgin saman Legas
Farashin saniya ya kai naira N2.5m, fiye da farashin mota a Legas, in ji mahauta
Wasu na da hannu a kashe-kashe domin neman shugabanci – Ministan Tsaron Nijeriya
NBC ta yi barazanar hukunta kafafen yaɗa labaran da suke saɓa ƙa’idojin aikin jarida a Nijeriya
Nijeriya na neman Turkiyya ta sasanta ta da Nijar don ƙarfafa hadin kai da yaƙi da ta’addanci
An ceto masu ciki da yara da dama daga wurin da ake haifar jarirai a sayar da su a Legas
Sojojin Nijeriya sun kama mutum 14 da ake zargi da satar mai a Jihar Legas
An sace dalibai da ke kan hanyarsu ta zuwa rubuta jarrabawar jami’a a Nijeriya
Harin Kasuwar Jilli ba kuskure ba ne – Ministan Tsaron Nijeriya ya kare matakin rundunar soji
Shuguba Tinubu ya rattaba hannu kan kasafin kudin Nijeriya na 2026, ya tsawaita wa'adin na 2025
Abin da ya sa Kungiyar Tuntuba ta Arewa ta ce Nijeriya ta shiga yanayi na yaƙi
Nijeriya ta yi gargaɗi kan 'shirin kai harin ta'addanci' kan kayayyakin more rayuwa a Abuja da Neja
Kamfanonin jiragen saman Nijeriya sun yi barazanar dakatar da aiki saboda tashin farashin man jirgi
NACA ta yi gargadi game da yaɗa bayanan HIV ba bisa ƙa'ida ba a shafukan sada zumunta a Nijeriya
Gwamnatin Nijeriya ta ce jihohi 33 da al'ummomi 14,000 na cikin hadarin ambaliyar ruwa a 2026
Dakarun Nijeriya sun kai samame a sansanin 'yanta'addan IPOB
'Yansanda a Nijeriya sun kama mutum 33 kan zargin satar mutane a coci
Turkiyya ta raba tallafin tan 36 na abinci ga 'yan gudun hijira a Nijeriya
Tana ƙasa tana dabo game da yiwuwar babban taron Jam'iyyar ADC a Nijeriya
'Yanta'adda sun kai hari sansanin sojin Nijeriya, sun kashe kwamanda da sojoji shida