| Hausa
KASUWANCI
3 minti karatu
Ana sa ran kasuwanci tsakanin Turkiyya da Nijeriya ya kai dala biliyan 10 saboda sabbin yarjeniyoyi
Manyan 'yan kasuwa sun ce ziyarar Shugaba Tinubu zuwa Turkiyya ta buɗe damarmaki a fannonin tsaro, ilimi, da masana'antu.
Ana sa ran kasuwanci tsakanin Turkiyya da Nijeriya ya kai dala biliyan 10 saboda sabbin yarjeniyoyi
Cinikin shekara-shekara tsakanin Turkiyya da Najeriya a halin yanzu ya kai kimanin dala biliyan 2, amma kasashen biyu na da burin kaiwa dala biliyan 10 zuwa shekarar 2026. / User Upload

Dangantakar kasuwanci da zuba jari tsakanin Nijeriya da Turkiyya na kan hanyar faɗaɗa cikin sauri, bayan rattaba hannu kan fiye da yarjejeniyoyi tara a yayin ziyarar shugaban Nijeriya, Bola Ahmed Tinubu a Turkiyya, in ji Dele Oye, shugaban Hukumar Kasuwancin Nijeriya da Turkiyya.

Yayin da yake magana da Anadolu, Oye ya ce yarjejeniyoyin sun shafi ilimin manyan makarantu da na gaba, tsaro, kasuwanci, tsara al'ummar ƙasa a ƙasashen waje, kayayyakin halal, da sauran muhimman sassa, duka ana ana sa ran za su sauƙaƙa kasuwanci da ayyuka ga kamfanonin Turkiyya a Nijeriya.

“Waɗannan yarjejeniyoyi za su faɗaɗa fagen aiki kuma su sauƙaƙa harkokin kamfanonin Turkiyya da ke son zuba jari da yin kasuwanci a Nijeriya,” in ji Oye.

Ya ce, Nijeriya, ƙasa mafi yawan al'umma a Afirka wadda ke da fiye da mutane miliyan 230, tana ba da babbar kasuwa ta masu amfani da kaya, kuma dandali ne mai muhimmanci don samun damar shiga kasuwannin nahiyar.

Masu AlakaTRT Afrika - Ziyarar Tinubu a Turkiyya: Muhimman abubuwa a tsarin dangatakar Nijeriya

“Nijeriya na ba da babbar kasuwa da kuma ƙofa zuwa Afirka,” in ji Oye, yana nuni da kasancewar kasar mamba a Shirin Yarjejeniyar 'Yancin Kasuwanci ta Nahiyar Afirka (AfCFTA), wadda ke ba da damar shiga kasuwar fifiko mai mutane biliyan 1.3.

Ya kuma ambata hulɗar kasuwanci ta musamman da China ta kulla da ƙasashe 53 na Afirka a 2025, yana cewa kamfanonin Turkiyya da ke aiki a Nijeriya za su iya amfani da ƙasar a matsayin gada don cinikayya da China.

“Saboda haka, babbar dama ce ga kamfanonin Turkiyya su kafa aiki a Nijeriya, su yi amfani da Nijeriya a matsayin ƙofa don shiga kasuwannin Afirka,” in ji shi.

Tallafin Turkiyya ga tsaron Nijeriya

Hulɗar tsaro ta kasance wani muhimmi ginshiƙi na dangantakar. Oye ya yi godiya ga Turkiyya kan goyon bayanta wajen magance matsalolin tsaro na Nijeriya, yana mai cewa ministan tsaron Nijeriya da manyan hafsoshin soji suna cikin tawagar shugaban ƙasa.

“A halin yanzu, Turkiyya na samar da jiragen sama, helikofta da kuma manyan kayayyakin masana'antu da dama zuwa Nijeriya. Mun zo nan ne don gina wannan haɗin-gwiwa domin mu ƙara faɗaɗa kasuwanci,” in ji shi.

Oye ya ce ƙasashen biyu sun kafa Kwamitin Haɗin-Gwiwa Mai Ƙarfi kan Tattalin Arziƙi da Kasuwanci, wanda ke nufin rage haɗarin zuba jari da inganta damar shiga kasuwa.

Burin dala biliyan 10

Adadin ciniki na shekara-shekara tsakanin ƙasashen ya kai dala biliyan 2 a halin yanzu, amma zai iya wuce dala biliyan 10 nan da 2026, in ji shi, yana danganta hakan ga tasirin sabbin yarjejeniyoyin suka samar.

“Babu gida a Nijeriya da ba shi da kaya samfurin Turkiyya,” in ji Oye, yana bayyana hangen nesa na ƙarin zurfafan hulɗar tattalin arziƙi da cewa “mai kyau ce, mai kyau ce, mai kyau ce.”

Ya ƙara da cewa gyare-gyaren tattalin arziƙin Nijeriya da ake aiwatarwa suna fara nuna sakamako, inda aka samu ribar ciniki a cikin shekaru biyu da suka gabata da kuma dakatar da matsalar giɓin ciniki na dindindin.

Banda tattalin arziƙi, Oye ya ce dangantaka tsakanin Nijeriya da Turkiyya tana ƙarfi a fannonin siyasa, al'adu, da diflomasiyya, abin da ya samu ƙarfin-gwiwa daga rashin kasancewar tarihin mulkin mallaka tsakanin ƙasashen biyu.

“A gare mu a Nijeriya, za a iya ɗaukar Turkiyya a matsayin gida na biyu. Haka kuma, Nijeriya na iya zama gida na biyu ga kamfanonin Turkiyya,” in ji shi, yana neman kamfanoni su amfana daga abin da ya kira hanyar maraba ta musamman daga gwamnatocin biyu.

Rumbun Labarai
Shigar kuɗaɗe daga waje cikin Nijeriya don zuba jari ta ƙaru da kusan kashi 90% a 2025 – Hukumomi
Hauhawar farashin mai ta janyo aiki daga gida da karatu daga nesa a wasu ƙasashen Asiya
Harin da aka kai wa 'yan kasuwar Ghana a Burkina Faso ya sa farashin tumatur ya tashi
Naɗin 'ya'yan Dangote mata uku a manyan muƙamai: Sabon babi a tsarin gado na kasuwancin iyali
China za ta soke karɓar harajin fitar da kayayyaki daga ƙasashen Afirka 53
Me ya sa farashin zinare ke tashi a lokacin rikicin siyasa a duniya?
Gwamnatocin Afirka sun juya ga tsarin Bankin Musulunci bayan nasarar Sukuk a Benin
Afrika na amfani da tagomashin da zinari yake samu don ƙara ƙarfin arziƙinta
Ghana ta biya basussukan dala biliyan 1.47 na fannin makashi da ake bin ta
Trump ya ce Amurka za ta karɓi gangar ɗanyen mai miliyan 50 daga Venezuela
Kamfanin Dangote ya yi watsi da ikirarin rufe matatar mansa
Me ya sa hanyoyin teku da aka toshe ke tayar da kura a Gabashin Afirka?
ECOWAS za ta cire harajin tafiye-tafiyen jiragen sama tsakanin ƙasashen Yammacin Afrika a 2026
Manyan ƙere-ƙeren fasaha na Afirka da suka yi tasiri a duniya
Abu biyar da ya kamata ku sani kan Taron G20 na farko a Afirka
An cire Nijeriya daga jerin kasashen da ake sa wa ido kan safarar kudade ba bisa ka'ida ba a duniya
Bai kamata kasuwanci da Afirka ya zama buƙatar ɗiban ma’adanai ba: Ministan Nijeriya Tuggar
Jamhuriyar Nijar ta kafa cibiyar tsaron intanet
Kamfanin simintin Dangote ya fara aiki a ƙasar Ivory Coast
Ana hasashen mambobin OPEC+ za su ƙara yawan fetur ɗin da suke fitarwa yayin da farashinsa ke karewa