Shugaban Amurka Donald Trump ya ce tsagaita wuta da Iran ta "zo ƙarshe" bayan sabbin hare-haren da Amurka ta kai, amma ya ce tattaunawar za ta iya ci gaba duk da sake ɓarkewar faɗa bayan hare-haren da Iran ta kai wa jiragen ruwa a Mashigar Hormuz.
"A ganina, ta ƙare," in ji Trump a taron NATO da aka yi a Ankara ranar Laraba lokacin da aka tambaye shi ko yarjejeniyar tsagaita wutar tana aiki har yanzu, inda ya kada baki ya ce "Ɓata lokaci ne tsaya wa ana mu’amala da su".
"Zan bar masu tattaunawarmu su ci gaba da tattaunawa idan suna so, amma ban ga hakan ba. Ba na son waɗannan mutane."
Farashin mai ya tashi da kashi biyar cikin ɗari bayan kalaman na Trump.
Ɓangarorin Iran da Amurka sun ba da rahoton kai hari kan wurare da dama, lamarin da ya sanya matsin lamba kan yarjejeniyar wucin-gadi don kawo ƙarshen yakinsu da kuma tura farashin mai zuwa matsayi mafi girma a cikin makonni biyu.
Kafafen watsa labaran gwamnatin Iran a ranar Laraba sun ba da rahoton fashewar abubuwa a kusa da Mashigar teku ta Hormuz, ciki har da shida a tsibirin Qeshm, bakwai a Birnin Sirik da kuma wasu a babban birnin Bandar Abbas mai tashar jiragen ruwa.
Daga baya kuma an bayar da rahoton fashewar wasu bama-bamai a birnin Bushehr mai tashar jiragen ruwa, wanda a nan ne tashar samar da wutar lantarki ta farar hula ta ƙasar ta ke, kuma tana kusa da tsibirin Kharg, babbar tashar mai inda kashi 90 cikin 100 na jigilar danyen mai na ƙasar ke gudana.
Kafafen watsa labarai na gwamnati sun ce an kashe wani mamba na rundunar sojojin juyin-juya-hali a kudu maso yammacin Iran.
Kai wa tsarin tsaro na Iran hari
Rundunar Tsaron Amurka ta ce dakarunta sun kai hari kan wurare sama da 80, ciki har da na'urorin tsaron sararin samaniyar Iran, da cibiyoyin radar bakin teku da kuma ƙananan jiragen ruwa 60 na dakarun Juyin-Juya-Hali.
Hare-haren na da manufar "rage ƙarfin Iran wajen ci gaba da kai hare-hare kan harkokin kasuwancin ƙasa da ƙasa da ke gudana ta hanyar cinikayyar ƙasa da ƙasa", in ji rundunar.
Martanin Tehran ya zo da sauri, inda dakarun Juyin-Juya-Hali suka ce sun kai hari kan cibiyoyin sojojin Amurka da dama a Kuwait da Bahrain, inda wani ɗan jaridar AFP ya ji ƙarar fashewar bama-bamai.
A safiyar Laraba, Ma'aikatar Harkokin Cikin Gida ta Bahrain da rundunar sojin Kuwait duk sun bayar da rahoton cewa an kunna tsarin tsaron sararin samaniyarsu, amma ba su bayar da cikakken bayani game da duk wata ɓarna da ka iya faruwa ba.
‘Manyan’ karya yarjejeniya
Babban mai shiga tsakani na Iran, Mohammad Bagher Ghalibaf, ya zargi Amurka da "saɓawa" yarjejeniyar fahimtar juna, ciki har da sake maido da takunkumin mai da kuma "keta sauye-sauyen da Iran ke yi a mashigar ruwan".
Washington ta soke takunkumin da ta ƙaƙaba wa sayar da man Iran, wanda hakan ya ƙara matsin lamba ga Tehran yayin da take tattaunawa kan sulhun ƙarshe game da rikicin.
Ma'aikatar Baitulmalin Amurka ta soke lasisin da aka sanar a watan Yuni wanda ya bai wa Iran damar samarwa, sayarwa da kuma isar da ɗanyen mai da kayayyakin da suka shafi hakan har zuwa ranar 21 ga watan Agusta.
"Ayyukan Iran a mashigar ruwa ba su dace da Amurka ba kwata-kwata kuma za a gamu da sakamako," in ji wani jami'in Amurka da ya tattauna da AFP.
Jami'in, wanda ya yi magana ba tare da an ambaci sunansa ba, ya ce yarjejeniyar fahimtar juna tsakanin Amurka da Iran "ta dogara ne kawai da aiki", yana mai gargadin cewa Tehran za ta ga fa'idoji ne kawai idan ta nuna "halayen kirki".

















