| Hausa
DUNIYA
2 minti karatu
Wani sanatan Amurka ya yi gargaɗi kan ƙaruwar ƙyamar Musulunci da ƙin jinin Larabawa
"Ya zama wajibi a gare mu duka mu kawo ƙarshen wannan shirun mu kuma yi tur da babbar murya kan ƙyamar Musulunci da ƙin jinin Larabawa," in ji Mark Warner.
Wani sanatan Amurka ya yi gargaɗi kan ƙaruwar ƙyamar Musulunci da ƙin jinin Larabawa
Yayin da ake sa ran watan Ramadan mai tsarki mai zuwa, Warner ya bukaci a sake jajircewa wajen fuskantar tsattsauran ra'ayi da nuna bambanci. / Reuters
13 Janairu 2026

Wani Sanatan Amurka Mark Warner a ranar Litinin ya ce Amurka na fuskantar ƙaruwar wariya ta addini da kuma tashin hankali mai cike da ƙiyayya, yana zargin gwamnatin Trump da taka rawa wajen ƙara yaduwar ƙiyayyar Musulmai da kuma ra'ayin ƙin Larabawa.

Warner ya ce ya yi magana a gaban Majalisar Dattawa domin yin Allah wadai da ƙaruwar ƙyamar addini da ƙiyayya mai tsanani da Amurkawa ke nunawa, tare da jan hankali kan yadda mulkin Trump ya rura wutar ƙyamar Musulunci da ƙin jinin Larabawa.”

"A yau na tsaya nan musamman don yin Allah wadai da wariyar da al'ummominmu na Musulmai da Larabawa 'yan Amurka ke fuskanta, kuma abin takaici ganin yadda Shugaban Ƙasar nan ɓaro-ɓaro yake nuna goyon bayan nuna wariya da ƙin jinin Musulunci,” in ji Sanatan.

A matsayin misali, Warner ya nuna maganganun da Shugaba Donald Trump ya yi a wani zaman Majalisar Bakanoni a watan da ya gabata game da mutane ‘yan asalin Somali, inda ya kira al'ummar da 'shara' kuma ya ce, 'Ba ma son su a ƙasarmu.'

Warner ya ce ya kira maganganun Trump 'masifa, da rage darajar ɗan’adam, kuma suna saɓa wa ƙa'idodin Amurka', yana jaddada cewa ya kamata a yi Allah wadai da su da kakkausar murya, kana ya kamata dukkan jami'an gwamnati su yi tur da hakan.

Maganganu masu ƙona rai a Majalisar Dokoki

Sanatan ya kuma soki maganganun ƙona rai da ake yi a cikin Majalisar, yana mai cewa wani sanatan da bai bayyana sunansa ba kwanan nan ya bayyana Musulunci a matsayin 'addini mai guba' wanda 'hakan bai dace da ƙimominmu na Ƙasashen Yamma ba'.

"Dukkanmu musamman ma mu da muke yi aiki a matsayin wakilan al’umma, dole ne mu kawo ƙarshen wannan shiru kuma cikin ƙarfi da ƙuduri mu yi Allah wadai da ƙiyayyar da ake nuna wa Musulmai da kuma ƙyamar Larabawa," in ji Warner.

Da yake magana kan gabatowar wata mai tsarki na Ramadan, Warner ya yi kira ga sabunta ƙudurin tunkarar nuna bambanci da wariya.

"A wata mai zuwa ga 'yan’uwanmu Musulmai za su fara azumin Ramadan, musamman a wannan lokacin na tunani ... amma gaskiya, a duk tsawon shekara, ya kamata ya zama wajibi a gare mu mu kira dukkan nau'ikan son-kai da wariya ga kowace al'umma ta addini kuma mu tsaya tsayin daka don kare duk al'ummominmu daga rashin adalci," in ji shi.

Rumbun Labarai
Chadi za ta tura sojoji 750 domin yaƙar 'yandaban Haiti
Trump: Amurka na duba yiwuwar 'kammala' hare-haren soji kan Iran
NATO na fuskantar ‘mummunar makoma’ idan ƙasashenta suka ƙi taimaka wa Amurka a yaƙin Iran - Trump
Trump ya ce bai shirya yin yarjejeniya ba domin kawo ƙarshen yaƙin Iran
Tsarin kiwon lafiya a Gabas ta Tsakiya na fuskantar barazana yayin da rikici ke ƙara muni: WHO
Kusan rabin rahotannin kafafen watsa labaran Birtaniya kan Musulmi na dauke da nuna wariya
Mashigar Hormuz: Hanyar ruwan da za ta iya girgiza tattalin arzikin duniya
Dalilai huɗu da suka sa matasan Afirka suka fi lafiyar ƙwaƙwalwa a duniya
Musulmai a Turkiyya, Oman, Singapore, da Australia za su fara azumin Ramadan a ranar Alhamis
'Babu wani takamaiman abin da aka cim ma' a ganawar Trump da Netanyahu a kan Iran
An ci tarar ƙananan hukumomi 10 a Holland kan binciken al'ummomin Musulmai ba tare da saninsu ba
Trevor Noah: Trump ya yi barazanar maka mai gabatarwa a Gasar Grammy a Kotu
Saudiyya da Isra'ila za su Amurka don tattaunawa yayin da Trump ke tura jiragen yaƙi na ruwa Iran
WHO: Amurka ta fita daga Hukumar Lafiya ta Duniya bayan shekara 78
Masana kimiyya sun gano zanen shacin hannu 'mai shekara 67,800' a wani kogo a Indonesia
Ministan Wajen Saudiyya da takwarorinsa na Iran, Oman da Qatar sun tattauna kan zaman lafiyar yanki
Amurka ta dakatar da ba da bizar masu ƙaura ga 'yan Nijeriya da wasu ƙasashe 74
Trump ya saka harajin kashi 25 kan ƙasashen da ke kasuwanci da Iran
An katse intanet da wayoyin hannu a Iran
Matar shugaban Turkiyya ta gana da shugaban UNRWA kan shirin buɗe ofis a Ankara