| Hausa
DUNIYA
2 minti karatu
Amurka ta dakatar da ba da bizar masu ƙaura ga 'yan Nijeriya da wasu ƙasashe 74
Ma'aikatar Harkokin Wajen Amurka a ranar Litinin ta ce ta soke biza fiye da 100,000 tun bayan dawowar Trump, wani tarihi na shekara guda.
Amurka ta dakatar da ba da bizar masu ƙaura ga 'yan Nijeriya da wasu ƙasashe 74
Amurka ta dakatar da ba da bizar masu ƙaura ga 'yan Nijeriya da wasu ƙasashe 74 / Reuters
14 Janairu 2026


Amurka ta ce a ranar Laraba ta dakatar da aiwatar da bizar baƙi daga Nijeriya da wasu ƙasashe 74, matakin da Shugaba Donald Trump ya ɗauka kan baƙi da ke son zuwa Amurka.

"Ma'aikatar Harkokin Wajen Amurka ta dakatar da aiwatar da takardar izinin shigar ƙasar ga ƙasashe 75," in ji wani mai magana da yawun Ma'aikatar Harkokin Wajen Amurka.

Sakatariyar Yaɗa Labarai ta Fadar White House Karoline Leavitt ta wallafa a shafinta na X cewa ƙasashen da abin ya shafa za su haɗa da Somaliya - wadda Trump ya dinga caccakarta cikin yanayi mai tsananin a baya bayan nan bayan da aka samu baƙin-haure da badakalar kuɗi a Minnesota - da kuma Rasha da Iran.

Leavitt ya wallafa wani labari na gidan talabijin na Fox News wanda ya ce sauran kasashen da abin ya shafa za su hada da wasu kasashe da ke da dangantaka ta abokantaka da Amurka, ciki har da Brazil, Masar da Thailand.

Trump bai ɓoye burinsa na rage yawan shige da fice daga mutanen da ba 'yan asalin Turai ba. Ya bayyana 'yan Somaliya a matsayin "shara" waɗanda ya kamata su "koma inda suka fito" kuma maimakon haka ya ce yana maraba da 'yan yankin Scandinavia wato Denmark, Norway, da Sweden da ke ƙaura zuwa Amurka.

Ma'aikatar Harkokin Wajen Amurka a ranar Litinin ta ce ta soke biza fiye da 100,000 tun bayan dawowar Trump, wani tarihi na shekara guda.

Ma'aikatar Tsaron Cikin Gida ta ce a watan da ya gabata gwamnatin Trump ta kori fiye da mutum 605,000, kuma wasu miliyan 2.5 sun tafi da kansu.

Wannan sabon matakin bai shafi bizar yawon bude ido ko ta kasuwanci ba, duk da cewa gwamnatin Trump ta yi alƙawarin tantance tarihin duk masu neman shiga shafukan sada zumunta.

Rumbun Labarai
Chadi za ta tura sojoji 750 domin yaƙar 'yandaban Haiti
Trump: Amurka na duba yiwuwar 'kammala' hare-haren soji kan Iran
NATO na fuskantar ‘mummunar makoma’ idan ƙasashenta suka ƙi taimaka wa Amurka a yaƙin Iran - Trump
Trump ya ce bai shirya yin yarjejeniya ba domin kawo ƙarshen yaƙin Iran
Tsarin kiwon lafiya a Gabas ta Tsakiya na fuskantar barazana yayin da rikici ke ƙara muni: WHO
Kusan rabin rahotannin kafafen watsa labaran Birtaniya kan Musulmi na dauke da nuna wariya
Mashigar Hormuz: Hanyar ruwan da za ta iya girgiza tattalin arzikin duniya
Dalilai huɗu da suka sa matasan Afirka suka fi lafiyar ƙwaƙwalwa a duniya
Musulmai a Turkiyya, Oman, Singapore, da Australia za su fara azumin Ramadan a ranar Alhamis
'Babu wani takamaiman abin da aka cim ma' a ganawar Trump da Netanyahu a kan Iran
An ci tarar ƙananan hukumomi 10 a Holland kan binciken al'ummomin Musulmai ba tare da saninsu ba
Trevor Noah: Trump ya yi barazanar maka mai gabatarwa a Gasar Grammy a Kotu
Saudiyya da Isra'ila za su Amurka don tattaunawa yayin da Trump ke tura jiragen yaƙi na ruwa Iran
WHO: Amurka ta fita daga Hukumar Lafiya ta Duniya bayan shekara 78
Masana kimiyya sun gano zanen shacin hannu 'mai shekara 67,800' a wani kogo a Indonesia
Ministan Wajen Saudiyya da takwarorinsa na Iran, Oman da Qatar sun tattauna kan zaman lafiyar yanki
Wani sanatan Amurka ya yi gargaɗi kan ƙaruwar ƙyamar Musulunci da ƙin jinin Larabawa
Trump ya saka harajin kashi 25 kan ƙasashen da ke kasuwanci da Iran
An katse intanet da wayoyin hannu a Iran
Matar shugaban Turkiyya ta gana da shugaban UNRWA kan shirin buɗe ofis a Ankara