| Hausa
SIYASA
2 minti karatu
Kotun Ƙolin Nijeriya ta rusa babban taron PDP wanda aka zabi Kabiru Turaki a matsayin shugaba
Hukuncin mai rinjayen alkalai ya ƙara da cewa duk wanda ya aikata cin zarafin tsarin shari’a yana yin hakan ne cikin sa kansa a haɗari.
Kotun Ƙolin Nijeriya ta rusa babban taron PDP wanda aka zabi Kabiru Turaki a matsayin shugaba
Kotun Ƙolin Nijeriya ta rusa babban taron PDP wanda aka zabi Kabiru Turaki a matsayin shugaba / Others

Kotun Kolin Nijeriya ta yi watsi da ƙarar da Kwamitin Zartarwa na Ƙasa na Jam’iyyar PDP da ke ƙarƙashin jagorancin Taminu Turaki ya shigar.

A cikin hukuncin da aka yanke a ranar Alhamis, Mai Shari’a Stephen ya bayyana cewa taron ƙasa na PDP da aka gudanar a Ibadan, Jihar Oyo, a ranakun 15 da 16 ga watan Nuwamba na shekarar da ta gabata, ya saɓa wa hukuncin da ke akwai na Kotun Tarayya, wanda Mai Shari’a James Omotosho ya yanke.

Kotun Ƙoli ta soki ɓangaren da Turaki ke jagoranta bisa zuwa wata kotun dabana domin samun umarni, maimakon su ɗaukaka ƙara.

Ta bayyana wannan mataki a matsayin cin zarafin tsarin shari’a.

Hukuncin mai rinjayen alkalai ya ƙara da cewa duk wanda ya aikata cin zarafin tsarin shari’a yana yin hakan ne cikin sa kansa a haɗari.

Hukuncin mai rinjaye ya yi watsi da ƙarar saboda rashin cancanta.

Ɓangaren Turaki ya roƙi Kotun Koli da ta soke hukuncin Kotun Daukaka Ƙara wanda ya soke taron saboda ya saɓa wa umarnin kotu da ke aiki a lokacin.

Ta hannun lauyansu, Paul Erokoro (SAN), masu ƙarar sun nemi kotun ta tabbatar da taron tare da watsi da ƙarar da wani ɓangare mai hamayya da ke biyayya ga Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, ya shigar.

Sai dai waɗanda ake ƙara, ciki har da tsohon Gwamnan Jihar Jigawa, Sule Lamido, sun bayyana cewa rikicin ya wuce batun cikin jam’iyya, yana kuma da alaƙa da ƙin bin umarnin kotu mai inganci.