| Hausa
AFIRKA
1 minti karatu
An kawar da mazan jiyan Kamaru yayin da majalisar dokokin ta zaɓi sabbin shugabanni
Zaɓen sabbin shuwagabannin ya nuna muhimmin sauyi na shekarun shuwagabbin a cikin majalisun da kundin tsarin mulki ya bai wa damar gadar Shugaba Paul Biya.
An kawar da mazan jiyan Kamaru yayin da majalisar dokokin ta zaɓi sabbin shugabanni
Sabbin shugabannin majalisar dokokin suna matsayin iya gadar Shugaba Paul Biya. / Reuters / Reuters
18 Maris 2026

Majalisar dokokin Kamaru a ranar Talata ta zaɓi Theodore Datouo na jam’iyyar CPDM mai mulki a matsayin sabon shugabanta, kamar yadda kafar watsa labaran ƙasar CRTV ta ruwaito, lamarin da ya kawo ƙarshen jagorancin shekara 34 na shugaba mai barin gado Cavaye Yeguie Djibril, mai shekara 86.

Datouo, mai shekara 65, da Aboubakary Abdoulaye, mai shekara 64 -wani sarkin gargajiya mai ƙarfin faɗa a ji - an zaɓe su ne su jagoranci majalisar wakilai da majalisar dattawan ƙasar.

Abdoulaye ya gaji Marcel Niat Njifenji, mai shekara 91, a matsayin shugaban majalisar dattawa.

Naɗa sabbin shugabannin ya nuna muhimmin sauyi na shekarun shugabanni a cikin majalisun da kundin tsarin mulki ya bai wa damar gadar Shugaba Paul Biya.

Biya, mai shekara 93, shugaban ƙasar mafi yawan shekaru a duniya, ya lashe zaɓen wa’adi na takwas a kan karagar mulki a zaɓen da aka yi zargin tafka maguɗi a watan Oktoba.

Sake zaɓansa ya tsawaita mulkinsa na kusan shekara 44 kuma zai iya sa ya ci gaba da jagorantar ƙasar da ke samar da mai da koko a tsakiyar Afirka zuwa kusan shekaru 100 da haihuwa.

Rumbun Labarai
Nijar ta ƙaddamar da sabon katin ɗan ƙasa na zamani mai tambarin AES
Laifi mafi muni: AU ta nemi MƊD ta ɗauki mataki kan biyan diyyar cinikin bayi bayan MƊD ta tabbatar
Ghana ta sake yin bita kan tsarin yaƙi da ta’addanci sakamakon barazanar masu tsattsauran ra’ayi
Rasha ta yi iƙirarin cewa 'yan kwangilar sojin Faransa na da yawa a Afirka
Hukumomi a Nijar sun kama wani mutum a Zinder bisa zargin yawan kai wa 'mata' hari a kan babur
Me ya sa diyyar cinikin bayi da mulkin mallaka suka zama masu muhimmanci ga Afirka a 2026
Hatsarin jirgin ruwa ya yi ajalin mutane tara, wasu da dama sun ɓata a gaɓar tekun Djibouti
MDD ta ayyana cinikin bayi a Afirka a matsayin ‘laifi mafi muni ga ɗan'adam'
Shugaban Ghana ya faɗa a New York cewa Amurka tana goge tarihin baƙar-fata
Iskar kasar Chadi ce mafi muni da rashin inganci a Afirka a 2025 - Rahoto
Ranar Tarin Fuka ta Duniya: Yadda injinan GeneXpert suke sauya yaƙi da cutar TB a Togo da Congo
Ghana ta buƙaci taimakon MDD don warware batun cinikin bayi saboda ƙarfafa ƙoƙarin neman biyan diyya
Makomarmu ba ta sayarwa ba ce: Abin da ya sa dole matasan Afirka su nemi ba’asin haraji da cin bashi
Me ya sa yawancin tutocin kasashen Afirka suke da kamanceceniyar kaloli?
Aƙalla mutum 81 sun mutu cikin makonni sakamakon ambaliyar ruwa a Kenya
An kashe mutum 64, cikinsu har da ƙananan yara 13, a harin asibitin Sudan — WHO
Eid al-Fitr: Hotunan yadda aka yi bikin ƙaramar Sallah a ƙasashen Afirka
Nijeriya ta zama ta huɗu yayin da Sahel ke kan gaba a yawan kashe-kashe na ta'addanci —Rahoto
Yadda duniya ta rungumi shan gahawa kuma manoma a Afirka suke samun alheri
CAF ta ayyana Maroko a matsayin ƙasar da ta lashe Gasar AFCON 2025