| Hausa
DUNIYA
2 minti karatu
Macron ya ce Faransa na fama da gobarar daji mafi muni da ba a taɓa ganin irinta ba
"Makonni masu zuwa za su kasance masu matuƙar wahala, kuma dole ne mu dage," a cewar Shugaban Faransa Emmanuel Macron.
Macron ya ce Faransa na fama da gobarar daji mafi muni da ba a taɓa ganin irinta ba
Jimillar jami'an kashe gobara 84 ne suka jikkata yayin da suke kokarin shawo kan gobarar.

Shugaban Faransa Emmanuel Macron ya ce ƙasarsa tana fama da gobarar daji mafi muni "da ba a taɓa ganin irinta ba" kuma "makonni masu zuwa za su kasance masu matuƙar wahala" yayin da hukumomi ke ci gaba da ƙoƙarin shawo kan mummunar gobara a yankin kudu maso yamma.

"Makonni masu zuwa za su kasance masu matuaƙr wahala, kuma dole ne mu dage," in ji Macron yayin ziyarar da ya kai sashen ayyukan kashe gobara da ceto na ma'aikatar (CODIS) da ke Bordeaux a ranar Litinin.

Ya ƙara da cewa ba a taɓa ganin irin wannan mummunar gobara a Gironde ba "kwata-kwata."

Macron ya ce dole ne ƙasar ta ci gaba da ƙoƙarin kashe abin da ya bayyana a matsayin gobarar daji mafi muni a tarihi.

Masu AlakaTRT Afrika - Turai na babbakewa: Me muka sani zuwa yanzu?

Shugaban na Faransa ya gode wa jami’an kashe gobara da na farar-hula da ‘yansanda da na tsaro da sojoji da ma'aikatan kiwon lafiya, da ma’aikatan sa-kai da kuma manoma waɗanda suka taimaka wajen ci gaba da shawo kan lamarin.

Haka kuma, ya miƙa godiya ga ƙasashen Turai da suka taimaka wa Faransa, yana mai yabawa kan abin da ya bayyana a matsayin babbar hanya ta haɗin kai. 

"Na san rayuwa tana da wahala, ana cikin damuwa, an rasa amfanin gona, ga kuma man fetur na da tsada," in ji Macron. "Na san 'yan kwanakin nan sun kasance masu matuƙar wahala."

Macron ya yi ta'aziyya ga iyalan jami’an kashe gobara biyu da suka mutu a makon da ya wuce yayin da suke ƙoƙarin aikin kashe gobarar dajin, yana mai jajanta wa hukumar CODIS tare da gode wa jami'an agajin gaggawa saboda ci gaba da ƙoƙarinsu.

Ya ce nan gaba Faransa za ta sake dasa wa tare da farfaɗo da dazukanta ta wata hanya daban.

Gobarar dajin, wadda ta tashi a kusa da Saumos da ke yankin Gironde na Faransa a ranar Laraba ta ƙone kusan hekta 42,000 (kadada 103,784) kuma ta tilasta kwashe mutane fiye da 220,000 daga gidajensu.

Jimillar jami’an kashe gobara 84 ne suka jikkata yayin da suke ƙoƙarin shawo kan gobarar.

Kazalika, har yanzu gobarar tana ci gaba ci a yankin Haute-Corse, da Var da kuma Landes, yayin da hukumomi suka ce an shawo kan gobarar da ta tashi a yankin Hautes-Alpes.