Nijeriya ta daɗe tana fama da hare-haren 'yan bindiga da na ƙungiyoyin 'yan ta'adda irin su Boko Haram da ISWAP./Hoto:Rundunar 'yan sandan Benue

Gwamnatin Benue da ke tsakiyar Nijeriya ta ce mutum aƙalla 30 ne suka mutu sakamakon harin da wasu 'yan bindiga suka kai ranar Juma'a da daddare a wani ƙauyen na jihar.

Kwamishinan Watsa Labarai na jihar Matthew Aboh ne ya tabbatar da mutuwar mutum 30 a harin da 'yan bindiga suka kai a ƙauyen Ayati.

Sai dai wasu rahotanni sun ce waɗanda aka kashe za su kai 50.

Jihar Benue na fama da ƙarin hare-haren 'yan bindiga a baya bayan nan, waɗanda ake alaƙantawa da makiyaya.

A watan jiya, wani hari da 'yan bindiga suka kai a jihar ya yi sanadin mutuwar aƙalla mutum 25.

Nijeriya ta daɗe tana fama da hare-haren 'yan bindiga da na ƙungiyoyin 'yan ta'adda irin su Boko Haram da ISWAP.

AA