Lamine Zeine ya ce sun yi bakin kokarinsu domin yin sulhu da ECOWAS amma ta ki amincewa./Hoto:Reuters

Firaiministan Nijar ya soki kungiyar ECOWAS kan yin "zagon kasa" a yunkurin samun mafita a rikicin kasar bayan wakilanta sun kaurace wa taron da ya kamata su halarta a kasar ranar Alhamis.

"Yau, baya ga Togo da ta yarda ta zo wannan taro, abin takaici shi ne ECOWAS ba ta zo ba," in ji Ali Mahaman Lamine Zeine a wani taron manema labarai da ya gudanar a Yamai, wanda Ministan Harkokin Wajen Togo Robert Dussey ya halarta.

"Akwai masu yin zagon kasa a cikin wannan kungiyar watakila ma har da wasu kasashe da ke cikinta," a cewar Zeine a yayin da Dussey ya ki cewa uffan.

'Rashin adalci ne sanya mana takunkumai'

An tsara taron ne domin Nijar ta tattauna da wakilan ECOWAS kan yadda za a samu mafita game da takunkuman da kungiyar ta kakaba wa kasar bayan sojoji sun kifar da gwamnatin Mohamed Bazoum a watan Yulin da ya gabata.

Sojojin Nijar sun gayyaci wakilan kungiyar zuwa babban birnin kasar amma wakilin Togo ne kawai ya je.

Dussey ya je Yamai a watan jiya inda ya tattauna kan wa'adin mika mulkin kasar ga gwamnatin farar-hula kuma an tsara zai koma kasar tare da sauran wakilan ECOWAS da suka hada da takwaransa na kasar Saliyo Timothy Kabba.

"An sanya wa Nijar takunkumai ne domin a yi mata rashin adalci kuma babu wata doka da ta yarda da hakan. Mun yi bakin kokarinmu domin yin sulhu da su amma abin takaici sun ki amincewa," in ji Zeine.

TRT Afrika da abokan hulda