Akwai sojojin Amurka 1,000 a Nijar. Hoto: US Africa Command

Nijar ta ce nan ba da jimawa ba Amurka za ta gabatar da ƙudirin ficewa daga kasar da ke Yammacin Afirka, bayan da gwamnatin mulkin soja a Yamai ta ce ta janye daga yarjejeniyar hadin gwiwa da ta ƙulla da Washington a shekarar 2012.

Ministan Harkokin Cikin Gida na Jamhuriyar Nijar Janar Mohamed Toumba ya gana da Jakadiyar Amurka Kathleen FitzGibbon a ranar Laraba inda suka tattauna kan batun.

FitzGibbon ta shaida wa Ministan cewa ƙasarta ta “lura da matakin da Nijar ta dauka na ficewa daga yarjejeniyar soji, kuma za ta dawo da wani shiri” kan “hanyoyin fitar da” sojojin Amurka sama da 1,000 da ke da hedikwata a Nijar, in ji sanarwar ma'aikatar.

Sanarwar da Niamey ta bayar na ɓallewa daga Amurka ta zo ne a ranar Asabar bayan wata ziyarar kwanaki uku da wata babbar tawagar Amurka ta kai don sabunta hulda da gwamnatin mulkin soja.

'Amincewar ɓangare ɗaya'

A tsakiyar watan Maris ne Nijar ta ce Washington ta sanya yarjejeniyar hadin gwiwa ta shekarar 2012 ba tare da amincewar ɗaya ɓangaren ba.

An jibge sojojin Amurka a wani sansani da ke sahara na dala biliyan 100 don yaƙi da ta'addanci da ke addabar Yammacin Afirka.

Bayan da Janar Abdourahamane Tchiani ya yi juyin mulki a watan Yuli, gwamnatin ƙasar ta kori sojoji daga tsohuwar ƙasar da ta yi mata mulkin mallaka, Faransa, tare da neman zurfafa dangantakar soji da siyasa da Rasha.

Maƙwabtan Mali da Burkina Faso sun yi irin wannan yunƙuri inda suka shiga yarjejeniyar tsaro ta hadin gwiwa da Nijar, inda suka fice daga kungiyar ECOWAS ta Yammacin Afirka.

Tattaunawa a waya da Putin

Tchiani ya yi magana ta wayar tarho a ranar Talata da shugaban kasar Rasha Vladimir Putin don tattaunawa kan "ƙarfafa" yarjejeniyoyin tsaronsu bayan da Moscow ta sanar a tsakiyar watan Janairu aniyar ta na "kara habaka" hadin gwiwar soji.

Tawagar Rasha ma ta ziyarci Nijar a watan Disamban da ya gabata.

TRT Afrika