Saudiyya da Faransa sun jaddada goyon bayansu ga kafa ƙasar Falasɗinu tare da yin kira ga Isra'ila da ta janye daga dukkan yankunan Lebanon, a cewar wata sanarwa ta haɗin gwiwa da aka fitar a ƙarshen ziyarar aiki da Yarima Mai Jiran Gado na Saudiyya Mohammed bin Salman ya kai Faransa.
Wannan sanarwar ta biyo bayan tattaunawa tsakanin bin Salman da Shugaban Faransa Emmanuel Macron a birnin Paris, inda suka kuma jagoranci taron farko na Majalisar Muhimmin Haɗin gwiwar ta Saudiyya.
Shugabannin biyu sun jaddada cewa akwai hanyar haɗin gwiwa ta zaman lafiya a yankin bisa ga ikon mallakar ƙasa, dokokin ƙasa da ƙasa, da kuma hanyoyin diflomasiyya.
Diflomasiyyar Gabas ta Tsakiya
Dangane da Falasdinu, Riyadh da Paris sun yi watsi da yunƙurin da aka yi na gurgunta haƙƙin Falasdinawa na kafa ƙasa mai cin gashin kanta a kan iyakokin 1967, suna neman a kawo ƙarshen manufofin Isra'ila da ba sa bisa ƙa'ida, da kuma tashin hankalin ‘yan kama wuri zauna.
Sun kuma yi kira da a samar da sharuɗɗan da za su ba da damar tsagaita wuta mai ɗorewa a Gaza tare da taimakon jin kai ba tare da wata tangarɗa ba, yayin da suke goyon bayan sake fasalin Hukumar Falasdinu.
Dangane da Lebanon, ƙasashen biyu sun amince su ƙara himma wajen cim ma matsaya ta ƙarshe kuma sun yi kira da a aiwatar da cikakken kudurin Kwamitin Tsaro na Majalisar Dinkin Duniya mai lamba 1701, kwace makamai daga hannun ƙungiyoyin da ba na gwamnati ba, da kuma janyewar Isra'ila daga dukkan yankunan Lebanon.
Dangane da Iran, ɓangarorin biyu sun jaddada buƙatar cim ma matsaya game da shirin nukiliya na Tehran kuma sun yi kira ga Iran da ta ci gaba da haɗin gwiwa da Hukumar Makamashin Nukiliya ta Duniya.
Da suke tabo batun Syria, shugabannin sun yi alƙawarin tabbatar da kwanciyar hankali da farfaɗowar tattalin arzikin ƙasar kuma sun yi maraba da ƙirƙirar Majalisar Kasuwanci ta haɗin gwiwa tsakanin Saudiyya, Syria da Faransa.

















