| Hausa
NIJERIYA
2 minti karatu
Ɗumbin magoya bayan Kwankwasiyya sun halarci taron komawar Kwankwaso Jam'iyyar ADC
Tsohon Ministan Tsaron na Nijeriya ya yi rajista da jam’iyyar ADC kuma ya karɓi katin shaidar zama ɗan jam’iyya a Gidan Kwankwasiyya da ke kan titin Miller Road, Bompai, Kano.
Ɗumbin magoya bayan Kwankwasiyya sun halarci taron komawar Kwankwaso Jam'iyyar ADC
Kwankwaso ya tsaya takarar shugaban ƙasa a shekarar 2023, inda ya zo na huɗu. / Rabi'u Musa Kwankwaso Facebook
30 Maris 2026

Shugabannin jam’iyyar ADC da ɗumbin magoya baya, musamman daga Ƙungiyar Kwankwasiyya, sun halarci taron sauya sheƙar tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa na Jam’iyyar New Nigeria People’s Party (NNPP), Sanata Rabiu Kwankwaso inda ya koma Jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) a hukumance.

Tsohon Ministan Tsaron na Nijeriya ya yi rajista da jam’iyyar ADC kuma ya karɓi katin shaidar zama ɗan jam’iyya a Gidan Kwankwasiyya da ke kan titin Miller Road, Bompai, Kano.

Ya kuma sanar da sauya sheƙarsa a shafinsa na X.

 “Sabuwar Asubahi. Mu ne ADC,” in ji tsohon gwamnan a ranar Litinin.

Daga cikin manyan mutanen da suka halarci taron akwai tsohon Shugaban Majalisar Dattawa kuma Shugaban jam’iyyar ADC na ƙasa, David Mark; Sakataren jam’iyyar na ƙasa kuma tsohon Ministan Harkokin Cikin Gida, Rauf Aregbesola; da kuma tsohon gwamnan jihar Anambra, Peter Obi.

Sauran sun haɗa da tsohon gwamnan jihar Sokoto, Sanata Aminu Tambuwal; tsohon Ministan Sufuri, Rotimi Amaechi; Sanata Dino Melaye; tsohon Shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, Cif John Odigie-Oyegun; da kuma tsohon gwamnan jihar Imo, Emeka Ihedioha.

Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa Atiku Abubakar da tsohon gwamna Peter Obi, waɗanda manyan abokan hamayyar Tinubu ne sun zama fuskar Jam’iyyar ADC.

Kwankwaso ya tsaya takarar shugaban ƙasa a shekarar 2023, inda ya zo na huɗu. Abubakar da Obi sun zo na biyu da na uku bi da bi.

A ranar Lahadi, Kwankwaso ya sanar da cewa ba kawai zai sauka daga shugabancin NNPP ba, har ma zai fice daga jam’iyyar gaba ɗaya, yana mai cewa “halin da siyasar ƙasar ke ciki a yanzu” na buƙatar “sake tsara tafiya bisa dabara.”

Wannan sauyi ya zo ne ƙasa da shekara guda kafin babban zaɓen Nijeriya na gaba. Jam’iyya mai mulki ta amince da Shugaba Tinubu ya nemi wa’adi na biyu a zaɓen Janairu na 2027, kuma ana sa ran zai tsaya takara.

 

 

Rumbun Labarai
Sojojin Nijeriya sun daƙile harin ISWAP, sun kashe ‘yanta’adda 38 a Borno
APC ta kammala babban taronta na ƙasa, Nentawe Yilwatda zai ci gaba da zama shugaban jam'iyyar
Nijeriya ta ƙaddamar da shirin riga-kafin HIV, na allurar Lenacapavir
NCC za ta toshe layukan waya masu alaka da damfara a Nijeriya
Nijeriya ta sassauta dokokin kuɗaden waje, kamfanonin man ƙetare za su iya fitar da duk kuɗaɗensu
'Yanta'addan Lakurawa sun kashe sojoji 11 da ɗansanda a harin kwanton-ɓauna a Jihar Kebbin Nijeriya
Sojojin ruwan Nijeriya sun kama masu tserewa Turai a ɓoye ta jirgin ruwa a Legas
NEMA ta karɓi 'yan Nijeriya 708 da suka maƙale a Jamhuriyar Nijar
Zarge-zargen da hukumar ICPC ke yi wa Nasir El-Rufai
Jami’ar Bayero ta Kano ta kori ɗalibai 171 bisa laifin gabatar da takardun bogi
Kotu ta yi wa tsohon babban akantan Nijeriya ɗaurin shekara 72 a gidan yari kan damfarar N868m
Taron gwamnoni a Legas ne ya hana ni zuwa Bikin Hawan Nasarawa – Gwamnan Kano
Tashin farashin mai a Nijeriya ya yi ƙamari yayin da yaƙin Amurka da Isra'ila kan Iran ya ƙi ƙarewa
Amurka ta tura jirage marasa matuƙa Nijeriya don tattara bayanan sirri kan 'yanta'adda
Sarki Charles ya amince da ‘mummunan’ mulkin mallakar da Birtaniya ta yi wa Nijeriya
Sarki Charles ya karɓi baƙuncin Shugaba Tinubu a ziyara mai tarihi a Birtaniya
Dakarun Nijeriya sun kashe 'yanta'adda 61 a Malam Fatori da ke arewa maso gabashin ƙasar
Tinubu ya umarci masu riƙe da muƙaman siyasa da ke son tsayawa takara a zaɓen 2027 su ajiye aiki
Tinubu ya umarci manyan hafsoshin tsaron Nijeriya su koma Maiduguri da zama
Hare-haren ƙunar-baƙin-wake sun kashe mutum aƙalla 23 a birnin Maiduguri na Nijeriya