Nijar ta dakatar da kafofin watsa labarai guda 10 na Faransa, kasar da ta yi mata mulkin mallaka, tana cewa suna yin barazana ga zaman lafiyar jama'a.
Wani bayani da aka karanta a gidan talabijin na gwamnati a ranar Jumma'a ya ce hukumomin da aka dakatar sau da yawa sun watsa "abubuwan da ake ganin suna iya haddasa babbar barazana ga zaman lafiyar jama'a, haɗin kan ƙasa, zamantakewa da dorewar daidaiton hukumomin" Nijar.
A cikinsu akwai France 24, Radio France Internationale, France Afrique Media, LSI Africa, Agence France-Presse, TV5 Monde, TF1 Info, Jeune Afrique da Mediapart.
An ce dakatarwar za ta fara aiki "nan da nan" kuma ta shafi " tsarin tauraron dan’adam da sadarwar kebul da hanyoyin dijital da shafukan intanet da manhajojin wayar hannu".
Karuwar adawa da mulkin mallaka
An dakatar da RFI da France 24 'yan kwanaki bayan rikon mulkin soja a watan Yulin 2023 wanda ya kawo Janar Abdourahmane Tiani kan mulki.
A watan Disamban 2024, an dakatar da BBC ta Burtaniya.
A ranar Talata, ita ma Burkina Faso, abokiyar haɗin gwiwa ta Nijar da Mali cikin Kungiyar Haɗin Kan Kasashen Sahel (AES), ta haramta watsa tashar TV5 Monde.
Hukuncin Nijar ya zo 'yan kwanaki kafin babban taron koli tsakanin Faransa da kasashen Afirka a Kenya.
Adawa da Faransa na ƙaruwa a wasu kasashen Afirka da ta yi wa mulkin mallaka yayin da nahiyar ke zama sabon dandali na fafatawar diflomasiyya.










