| Hausa
SIYASA
2 minti karatu
Majalisar Dattijan Nijeriya ta amince da tsarin aika sakamakon zabe kai-tsaye ta intanet
Tun da fari an samu saɓanin ra'ayi tsakanin Majalisar Wakilai wacce ta yarda a sanya tsarin ya zama dole, da kuma Majalisar Dattawa wacce ta dage kan cewa hakan "zabi ne", ba wajibi ba.
Majalisar Dattijan Nijeriya ta amince da tsarin aika sakamakon zabe kai-tsaye ta intanet
Majalisar Dattijai / Nigerian Senate
10 Fabrairu 2026

Majalisar Dattijan Nijeriya ta amince da tsarin aikawa da sakamakon zabe kai-tsaye ta intanet, wanda ke cikin batun ƙudurin gyaran dokar zaɓe ta shekarar 2022.

Tun da fari an samu saɓanin ra'ayi tsakanin Majalisar Wakilai wacce ta yarda a sanya tsarin ya zama dole, da kuma Majalisar Dattawa wacce ta dage kan cewa hakan "zabi ne", ba wajibi ba.

Majalisar Dattawan ta amince ne bayan wani zaman gaggawa da ta yi a ranar Talata, saboda yadda batun ya tayar da jijiyoyin wuya a ƙasar.

Majalisar Dattijan ta ce aika sakamakon kai-tsaye ta na'ura zai kasance matakin farko na aika sakamakon, amma idan an samu matsalar intanet, INEC za ta yi amfani da rubutawa a takarda wajen aika sakamakon kamar yadda aka saba yi a baya.

Sanata Tahir Munguno ne ya gabatar da ƙudirin a lokacin zaman gaggawa da majalisa ta yi kan dokar, yayin da shugaban majalisar ya Godswill Akpabio ya amince da ƙudirin bayan amincewar sauran ƴanmajalisar.

Majalisar ta kuma kafa kwamiti mai mambobi 12 domin yin aiki da majalisar wakilai don yin nazarin dokokin kamar yadda tsarin amincewa da dokoki ya tanada.

Majalisar ta kira zaman gaggawar ne bayan da ƙungiyoyin fararen-hula da jam'iyyun hamayya suka mamaye harabar majalisar dattawan a ranar Litinin don yin zanga-zangar adawar da ƙin amincewa da majalisar ta yi na wajabta aikata sakamakon zaɓe ta na'ura kai tsaye daga kowace rumfar zaɓe.

 

Rumbun Labarai
Shugaban Nijar ya ziyarci Aljeriya, lamarin da ya nuna ƙarshen tsamin dangantaka tsakanin ƙasashen
Trump ya bar ƙofar Iran a bude, kuma Netanyahu ba zai iya rufe ta ba
Yadda 'yan Nijeriya suka fusata kan matakin Amurka na saka wa Kwankwaso takunkumi
Taƙaddama a kan gyaran dokar zaɓe ta Nijeriya
Ghana ta yi wa jakadanta a Nijeriya kiranye kan zargin maguɗin zaɓe
Iran ta ce ta shiga tattaunawar Oman da Amurka da 'kyakkyawar niyya'
Masar da Saudiyya sun yi kira ga samar da hanyoyin da suka dace kafin tattaunawar Amurka da Iran
Greenland ba hajar sayarwa ba ce
Yayin da duniya ta koma kasuwar buƙatar diflomasiyya, wai zai tsaya wa ƙasashe marasa ƙarfi a 2026?
Amurka ta dakatar da bai wa ‘yan Nijeriya biza
Alkawarin dala miliyan 150 zai sake gina Aleppo da yaƙi ya lalata
Yadda 'nadamar zalunci' ke janyo rushewar lafiyar ƙwaƙwalwa a rundunar sojin Isra’ila
Me ya sa Trump da masu sharhi da ke da ra’ayin rikau ke sa ido kan al’ummar Somalia da ke Minnesota?
Shugaban Nijar Tiani ya karɓi shugaban Bilma bayan ya yi watanni 16 a hannun masu garkuwa da mutane
An daƙile harin RSF kan West Kordofan: Rundunar Sojin Sudan
Nijar ta ce ta fara kai uranium ɗinta kasuwar duniya
Trump ya ce Amurka za ta dakatar da hijirar 'yan cirani daga kasashe marasa arziki har abada
Gobarar Hong Kong: Adadin waɗanda suka mutu ya kai 128 yayin da aka shiga kwana uku a ƙoƙarin ceto
China ta yi gargaɗin 'murƙushe' katsalandan ɗin ƙetare kan shirin makami mai linzani na Japan
Yaƙin Sudan: Maye gurbin UAE da Turkiyya na iya ƙarfafa ƙoƙarin ƙasashe na samar da zaman lafiya