Taƙaddama a kan gyaran dokar zaɓe ta Nijeriya
SIYASA
3 minti karatu
Taƙaddama a kan gyaran dokar zaɓe ta NijeriyaSai dai, babban abin da ya tada kura shi ne matakin da Majalisar Dattawa ta dauka na cire wani sashi mai muhimmanci a cikin dokar.
Shugaban Majalisar Dinkin Najeriya - Godswill Akpabio / Others
9 Fabrairu 2026

Wani batu da yake ci gaba da tayar da jijiyoyin wuya a fagen siyasar Nijeriya shi ne batun gyaran Dokar Zabe ta shekarar 2022. 'Yan Nijeriya da dama na fatan wannan gyara zai magance kura-kuran da aka samu a zabukan 2023.

Sai dai, babban abin da ya tada kura shi ne matakin da Majalisar Dattawa ta dauka na cire wani sashi mai muhimmanci a cikin dokar.

Babban abin da ya raba kawunan masu ruwa da tsaki shi ne batun wajabta aikawa da sakamakon zabe kai-tsaye ta intanet (electronic transmission).

Yayin da Majalisar Wakilai ta amince da sanya hakan a matsayin "tilas", ita kuwa Majalisar Dattawa ta dage kan cewa hakan "zabi ne", ba wajibi ba.

Wannan matsayar ta Majalisar Dattawa ta sa Kungiyar Kwadago ta Kasa (NLC) gudanar da zanga-zanga a gaban Majalisar Dokoki da ke Abuja a ranar Litinin, domin matsa lamba ga sanatocin su sauya matsayarsu.

Masu fafutika na ganin cewa ƙin wajabta aikawa da sakamakon zaben zai rage kwarin gwiwar jama'a kan sahihancin zaben 2027.

Suna zargin cewa barin batun a matsayin "zabi" zai iya zama wata kafa ta tafka maguɗi, musamman a matakan tattara sakamako (collation centers) inda aka saba samun matsaloli.

An kwashe shekaru masu yawa ana yin zaɓuka a Nijeriya, sai dai galibi zarge-zargen magudi suna dabaibaye tsarin ne musamman a lokacin tattara sakamako.

A mafi yawan lokuta, mutane suna kaɗa ƙuri’unsu ne cikin lumana a rumfunan zaɓe, amma matsalar tana farawa ne lokacin aikawa da sakamakon daga wata cibiyar tattara sakamakon zuwa wata.

A wannan gaɓar ne ake zargin ana samun sauya alkaluma ko ɓatan sakamako na gaskiya.
Hakan ce ta sa a ƙoƙarin magance magudi kafin zaɓukan 2023, Hukumar INEC ta gabatar da na'urar BVAS da shafin IReV.

Tsarin IReV (INEC Result Viewing Portal) wani babban shafin intanet ne da aka samar domin:

Dakile aringizon kuri'u.

Inganta gaskiya da amana.

Wallafa hoton takardar sakamakon zaɓe (Form EC8A) kai-tsaye daga rumfar zaɓe.

Bai wa kowane ɗan ƙasa damar ganin sakamakon kowace rumfa ta wayarsa ko kwamfuta a duk inda yake.

Tabbatar da cewa abin da aka bayyana a rumfar zaɓe, shi ne abin da zai je babban shafin hukumar ba tare da an sauya shi a hanya ba.

Manufar ita ce: da zarar an kammala ƙidaya ƙuri'u a rumfar zabe, jami'ai za su tura sakamakon kai-tsaye zuwa shafin intanet domin kowa ya gani.

Duk da cewa Majalisar Dattawa ta tafi hutun mako biyu bayan amincewa da dokar a makon jiya, shugabancin majalisar ya kira wani taron gaggawa a ranar Talata.

Kodayake ba a bayyana dalilin taron ba, ana kyautata zaton za a sake nazarin wannan sashi na aikawa da sakamako ne sakamakon matsin lamba daga jama'a.

Masana na nan akan bakarsu cewa: muddin aka wajabta tura sakamako daga rumfunan zabe zuwa shafin IReV, za a rage kura-kuran da suka dabaibaye harkar zabe a Nijeriya tsawon shekaru.

Rumbun Labarai
Shugaban Nijar ya ziyarci Aljeriya, lamarin da ya nuna ƙarshen tsamin dangantaka tsakanin ƙasashen
Trump ya bar ƙofar Iran a bude, kuma Netanyahu ba zai iya rufe ta ba
Yadda 'yan Nijeriya suka fusata kan matakin Amurka na saka wa Kwankwaso takunkumi
Majalisar Dattijan Nijeriya ta amince da tsarin aika sakamakon zabe kai-tsaye ta intanet
Ghana ta yi wa jakadanta a Nijeriya kiranye kan zargin maguɗin zaɓe
Iran ta ce ta shiga tattaunawar Oman da Amurka da 'kyakkyawar niyya'
Masar da Saudiyya sun yi kira ga samar da hanyoyin da suka dace kafin tattaunawar Amurka da Iran
Greenland ba hajar sayarwa ba ce
Yayin da duniya ta koma kasuwar buƙatar diflomasiyya, wai zai tsaya wa ƙasashe marasa ƙarfi a 2026?
Amurka ta dakatar da bai wa ‘yan Nijeriya biza
Alkawarin dala miliyan 150 zai sake gina Aleppo da yaƙi ya lalata
Yadda 'nadamar zalunci' ke janyo rushewar lafiyar ƙwaƙwalwa a rundunar sojin Isra’ila
Me ya sa Trump da masu sharhi da ke da ra’ayin rikau ke sa ido kan al’ummar Somalia da ke Minnesota?
Shugaban Nijar Tiani ya karɓi shugaban Bilma bayan ya yi watanni 16 a hannun masu garkuwa da mutane
An daƙile harin RSF kan West Kordofan: Rundunar Sojin Sudan
Nijar ta ce ta fara kai uranium ɗinta kasuwar duniya
Trump ya ce Amurka za ta dakatar da hijirar 'yan cirani daga kasashe marasa arziki har abada
Gobarar Hong Kong: Adadin waɗanda suka mutu ya kai 128 yayin da aka shiga kwana uku a ƙoƙarin ceto
China ta yi gargaɗin 'murƙushe' katsalandan ɗin ƙetare kan shirin makami mai linzani na Japan
Yaƙin Sudan: Maye gurbin UAE da Turkiyya na iya ƙarfafa ƙoƙarin ƙasashe na samar da zaman lafiya