| Hausa
SIYASA
1 minti karatu
Ghana ta yi wa jakadanta a Nijeriya kiranye kan zargin maguɗin zaɓe
Matakin ya biyo bayan zarge-zargen sayen ƙuri'u ne yayin zaɓen fid da gwani na 'yan majalisu a Jam'iyyar NDC.
Ghana ta yi wa jakadanta a Nijeriya kiranye kan zargin maguɗin zaɓe
Shugaba Mahama ya sa an yi wa Ahmed kiranye ne sakamakon rawar da ake zargin ya taka a maguɗin zaɓe a matsayinsa na jam’in gwamnati. / AFP
9 Fabrairu 2026

Shugaba John Mahama na Ghana ya yi wa jakadan ƙasar a Nijeriya, Baba Ahmed, kiranye bisa zargin hannu a maguɗin zaɓe a zaɓen fid da gwani na ‘yan majalisu a mazaɓar Ayawaso East.

Wata sanarwa da fadar Shugaban ƙasar Ghana ta fitar a Accra ta bayyana cewa an yi Ahmed, wanda ya kasance mai neman takara, kiranye ne sakamakon rawar da ake zargin ya taka a maguɗin zaɓe a matsayinsa na jam’in gwamnati.

Sanarwar ta ce kiranye zai yi aiki ne nan-take, kuma an ɗauki matakin ne domin kauce wa duk wani tunanin rashin adalci ko kuma saɓa wa dokar ɗa’ar ma’aikata ga waɗanda aka bai wa muƙaman siyasa.

Ta jaddada cewa ci gaba da zamansa a ofishin abu ne da ba zai yiwu ba a irin wannan yanayi.

An zargi masu neman takara a zaɓen fid da gwani da laifin sayen ƙuri’u.

Rumbun Labarai
Shugaban Nijar ya ziyarci Aljeriya, lamarin da ya nuna ƙarshen tsamin dangantaka tsakanin ƙasashen
Trump ya bar ƙofar Iran a bude, kuma Netanyahu ba zai iya rufe ta ba
Yadda 'yan Nijeriya suka fusata kan matakin Amurka na saka wa Kwankwaso takunkumi
Majalisar Dattijan Nijeriya ta amince da tsarin aika sakamakon zabe kai-tsaye ta intanet
Taƙaddama a kan gyaran dokar zaɓe ta Nijeriya
Iran ta ce ta shiga tattaunawar Oman da Amurka da 'kyakkyawar niyya'
Masar da Saudiyya sun yi kira ga samar da hanyoyin da suka dace kafin tattaunawar Amurka da Iran
Greenland ba hajar sayarwa ba ce
Yayin da duniya ta koma kasuwar buƙatar diflomasiyya, wai zai tsaya wa ƙasashe marasa ƙarfi a 2026?
Amurka ta dakatar da bai wa ‘yan Nijeriya biza
Alkawarin dala miliyan 150 zai sake gina Aleppo da yaƙi ya lalata
Yadda 'nadamar zalunci' ke janyo rushewar lafiyar ƙwaƙwalwa a rundunar sojin Isra’ila
Me ya sa Trump da masu sharhi da ke da ra’ayin rikau ke sa ido kan al’ummar Somalia da ke Minnesota?
Shugaban Nijar Tiani ya karɓi shugaban Bilma bayan ya yi watanni 16 a hannun masu garkuwa da mutane
An daƙile harin RSF kan West Kordofan: Rundunar Sojin Sudan
Nijar ta ce ta fara kai uranium ɗinta kasuwar duniya
Trump ya ce Amurka za ta dakatar da hijirar 'yan cirani daga kasashe marasa arziki har abada
Gobarar Hong Kong: Adadin waɗanda suka mutu ya kai 128 yayin da aka shiga kwana uku a ƙoƙarin ceto
China ta yi gargaɗin 'murƙushe' katsalandan ɗin ƙetare kan shirin makami mai linzani na Japan
Yaƙin Sudan: Maye gurbin UAE da Turkiyya na iya ƙarfafa ƙoƙarin ƙasashe na samar da zaman lafiya