| Hausa
GABAS TA TSAKIYA
3 minti karatu
Iran ta ce ta kai hari sansanin sojin Amurka da ke UAE, ta harbo jiragen leken asiri na ƙasar
Tehran ta ce jiragen samanta marasa matuƙa da dama sun kai hari kan ma'aikatan Amurka da tashar jiragen helikwafta a sansanin sojin saman Al Minhad a matsayin ramuwar gayya ga harin da Amurka ta kai kan tsibirin Larak na Iran.
Iran ta ce ta kai hari sansanin sojin Amurka da ke UAE, ta harbo jiragen leken asiri na ƙasar
Iran ta ce ta kai hari sansanin sojin Amurka da ke UAE, ta harbo jiragen leken asiri na ƙasar

Rundunar sojin Iran a ranar Litinin ta ce ta harbo jiragen sama marasa matuƙa da dama a sansanin sojin Amurka na Al Minhad da ke Hadaddiyar Daular Larabawa UAE, a wani mataki na ramuwar gayya ga harin da Amurka ta kai a Tsibirin Larak na Iran.

Rundunar sojin Iran ta ce harin ya nufi wuraren da ma'aikatan sojin Amurka da tashar jiragen helikwafta su ke a sansanin, wanda ta bayyana a matsayin muhimmin cibiyar jigilar kayayyaki da tashar jiragen sama ga sojojin kasashen waje, a cewar kamfanonin dillancin labarai na Iran.

Rundunar ta yi alƙawarin ɗaukar fansa kan sojojin Amurka, tana mai cewa wannan wani martani ne ga kisan da aka yi wa membobin rundunar kare juyin juya halin Iran da fararen hula a harin da Amurka ta kai ranar Lahadi. 

Rundunar ta ce ta harbo wani jirgin leken asiri na Amurka kirar MQ-9 Reaper a kan mashigar Hormuz da makami mai linzami, wanda hakan ya sa ya fado cikin ruwan Gulf, a cewar kamfanin dillancin labarai na Mehr na Iran.

Hakan ya biyo bayan harin da Amurka ta kai wa jiragen Iran biyu a Tsibirin Larak ranar Lahadi, wanda ya zama hari na farko da Amurka ta kai wa yankin Iran tun karshen watan Yuli, kamar yadda wani jami'in Amurka ya shaida wa Axios.

Haka kuma rundunar ta IRGC ta ce an kashe tare da jikkata wasu daga cikin mayakanta da fararen hula da dama a harin kuma ta yi alƙawarin ɗaukar fansa.

Kamfanin dillancin labarai na Tasnim na Iran ya ruwaito cewa bayanan farko sun nuna cewa jiragen sama marasa matuka na Amurka ne suka kai harin.

Pezeshkian ya yi alƙawarin ɗaukar fansa

Shugaban Iran Masoud Pezeshkian ya fada a ranar Litinin cewa, Tehran ba ta neman yaƙi amma ba za ta yi shiru ba idan aka tsokane ta.

Da yake magana kafin ya tafi Bishkek don halartar taron ƙungiyar haɗin gwiwa ta Shanghai (SCO), Pezeshkian ya ce Iran za ta mayar da martani mai muni ga duk wani hari da aka sake kai mata, a cewar kamfanin dillancin labarai na Fars.

"Rashin zaman lafiya da tashin hankali a yankin ba su da amfani ga kowace ƙasa kuma za mu ƙalubalanci kowa," in ji shi.

Hare-haren na baya-bayan nan sun zo ne a daidai lokacin da ake takun saka tsakanin Tehran da Washington, inda Iran ke barazanar ƙara ɗaukar fansa bayan harin da Amurka ta kai a Tsibirin Larak.

Rumbun Labarai
Shugaban Siriya ya naɗa tsohon shugaban ƙungiyar SDF/YPG a matsayin mai ba shi shawara
Babbar ɗimuwar Netanyahu: Mafarkin Turkiyya na shirin kai hari
Shugaban Iran ya yi kira ga ƙasashen Musulmai su daina bari ana kai hare-hare daga cikin ƙasashensu
Hare-haren Iran sun ragargaza cibiyoyin leken asirin Amurka a Gabas ta Tsakiya: Rahoto
Iran ta yi gargaɗin cewa yaƙi da Amurka nan gaba zai iya shafar duka shiyyar da ma fannin makamashi
Trump ya ce an cire abubuwan fashewa daga Mashigar Hormuz, ya gargaɗi Iran kan dasa wasu
Saudiyya da Faransa sun goyi bayan kafa ƙasar Falasɗinu, sun buƙaci Isra’ila ta janye daga Lebanon
Hantarar da Amurka ke yi mana za ta ta'azzara ƙoƙarin diflomasiyya, in ji Iran
Iran ta ci gaba da nuna rashin tsoro yayin da Amurka ke ci gaba da ƙara mata matsin lamba
Ya kamata yaƙi da Amurka ya ƙare yayin da Tehran ke da  'iko da mutunci': Pezeshkian
Sabbin takunkuman da Amurka ta saka mana ta'addanci ne a fannin tattalin arziki, in ji Iran
Tsohon Ministan Tsaron Isra'ila Yaalon ya zargi Netanyahu da neman rikici da Turkiyya
Ko dabarun yaƙi na Iran za su sanya Amurka sake tunani?
Iran na duba yiwuwar kai hari kan cibiyoyin sojin Amurka da ke Turai: Rahoto
Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa ta dakatar da kasuwanci da Iran har 'sai abin da hali ya yi'
Saudiyya ta yaba wa sabon ƙawancen tsaron teku da ya fara aiki
Iran ta ce ta yi nasara a 'yaƙi da kuma diflomasiyya' bayan Trump ya nemi a yi saranda
Trump ya yi barazanar kai wa Oman harin bam idan ta 'kawo cikas' a tattaunawar Amurka da Iran
'Ba za a iya ƙwace Hormuz ta saƙon X ko jirgin dakon jiragen yaƙi ko jawabin zaɓe ba' — Iran
Amurka da Iran sun amince su tsawaita wa'adin yarjejeniyar tsagaita wuta, in ji majiyoyin Pakistan