Rundunar sojin Iran a ranar Litinin ta ce ta harbo jiragen sama marasa matuƙa da dama a sansanin sojin Amurka na Al Minhad da ke Hadaddiyar Daular Larabawa UAE, a wani mataki na ramuwar gayya ga harin da Amurka ta kai a Tsibirin Larak na Iran.
Rundunar sojin Iran ta ce harin ya nufi wuraren da ma'aikatan sojin Amurka da tashar jiragen helikwafta su ke a sansanin, wanda ta bayyana a matsayin muhimmin cibiyar jigilar kayayyaki da tashar jiragen sama ga sojojin kasashen waje, a cewar kamfanonin dillancin labarai na Iran.
Rundunar ta yi alƙawarin ɗaukar fansa kan sojojin Amurka, tana mai cewa wannan wani martani ne ga kisan da aka yi wa membobin rundunar kare juyin juya halin Iran da fararen hula a harin da Amurka ta kai ranar Lahadi.
Rundunar ta ce ta harbo wani jirgin leken asiri na Amurka kirar MQ-9 Reaper a kan mashigar Hormuz da makami mai linzami, wanda hakan ya sa ya fado cikin ruwan Gulf, a cewar kamfanin dillancin labarai na Mehr na Iran.
Hakan ya biyo bayan harin da Amurka ta kai wa jiragen Iran biyu a Tsibirin Larak ranar Lahadi, wanda ya zama hari na farko da Amurka ta kai wa yankin Iran tun karshen watan Yuli, kamar yadda wani jami'in Amurka ya shaida wa Axios.
Haka kuma rundunar ta IRGC ta ce an kashe tare da jikkata wasu daga cikin mayakanta da fararen hula da dama a harin kuma ta yi alƙawarin ɗaukar fansa.
Kamfanin dillancin labarai na Tasnim na Iran ya ruwaito cewa bayanan farko sun nuna cewa jiragen sama marasa matuka na Amurka ne suka kai harin.
Pezeshkian ya yi alƙawarin ɗaukar fansa
Shugaban Iran Masoud Pezeshkian ya fada a ranar Litinin cewa, Tehran ba ta neman yaƙi amma ba za ta yi shiru ba idan aka tsokane ta.
Da yake magana kafin ya tafi Bishkek don halartar taron ƙungiyar haɗin gwiwa ta Shanghai (SCO), Pezeshkian ya ce Iran za ta mayar da martani mai muni ga duk wani hari da aka sake kai mata, a cewar kamfanin dillancin labarai na Fars.
"Rashin zaman lafiya da tashin hankali a yankin ba su da amfani ga kowace ƙasa kuma za mu ƙalubalanci kowa," in ji shi.
Hare-haren na baya-bayan nan sun zo ne a daidai lokacin da ake takun saka tsakanin Tehran da Washington, inda Iran ke barazanar ƙara ɗaukar fansa bayan harin da Amurka ta kai a Tsibirin Larak.























