| Hausa
GABAS TA TSAKIYA
3 minti karatu
Harin Amurka a Tsibirin Larak na Iran ya kashe mutane da dama da kuma jikkata wasu
Harin Amurka ya kashe mutane da dama tare da jikkata wasu dakarun Rundunar Juyin-Juya-Hali da kuma fararen hula, inda Iran ta yi alƙawarin ɗaukar fansa da "hukuncin mai tsauri," a cewar rundunar IRGC,
Harin Amurka a Tsibirin Larak na Iran ya kashe mutane da dama da kuma jikkata wasu
Harin Amurka a Tsibirin Larak na Iran ya kashe mutane da dama da kuma jikkata wasu

Wani hari da Amurka ta kai a Tsibirin Larak da ke kudancin Iran ya kashe mutane da dama tare da jikkata wasu dakarun Rundunar Kare Juyin-Juya-Halin (IRGC) da fararen hula da dama, a cewar dakarun, wadanda suka yi alƙawarin mayar da martani da "hukuncin mai tsauri".

A cikin wata sanarwa da aka fitar, sashen hulda da jama'a na IRGC ya zargi Amurka da kai hari "mai muni" a tsibirin da ke lardin Hormozgan a kudancin ƙasar a ranar Lahadi.

‘‘Abokan gaba na Amurka da Isra’ila wadanɗa suka gagara warware matsalolinsu na cikin gida da kuma raguwar aminci da suke da shi a tsakanin ƙasashe a yankin, a wani mataki na ƙoƙarin nuna rawar da suke takawa, sun kai wani mummunar hari Tsibirin Larak, inda suka kashe tare da jikkata mayakanmu da 'yan ƙasarmu da dama," in ji sanarwar.

A cikin wata sanarwa da kamfanin dillancin labarai na Fars na Iran ya fitar, mai magana da yawun IRGC, Sardar Mohebi, ya zargi Amurka da aikata "mummunan kuskure kuma mai hatsari", wanda zai haifar da sakamako "a fannin tattalin arziki da na soja".

Da farko dai, Fars ya ba da rahoton cewa mazauna yankin sun ji fashewar wani abu kusa da Tsibirin Larak, yayin da ba a tabbatar da ainihin wurin da abin ya faru ba.

Rahotanni daga Iran sun zo ne bayan da kafofin watsa labarai na Amurka suka ce sojojin Amurka sun kai hari kan tsibirin, inda aka bayyana yanda sojoji suke shirin harba rokoki da bama-bamai zuwa cikin Mashigar Hormuz.

Rundunar Sojin Amurka ta kammala wani aiki na kawar da nakiyoyin ruwa daga hanyoyin jigilar kaya na kasa da kasa ta hanyar mashigar ruwan a makon da ya gabata, a cewar gwamnatin Trump.

A ranar Talata shugaban Amurka Donald Trump ya bayyana cewa "An sanar da Iran cewa duk wani jirgi ko kwale-kwale da ke dauke da nakiya za a lalata shi nan take kuma cikin tsari."

"Sojojin Amurka suna sa ido sosai kan yankin kuma a shirye suke don kare 'yancin zirga-zirgar jiragen kasuwanci ta wannan muhimmin hanyar ruwa," a cewar wani jami'in Amurka.

Tun da farko, Kakakin Majalisar Dokokin Iran Mohammad Bagher Ghalibaf ya yi watsi da ikirarin Sakataren Baitulmalin Amurka Scott Bessent kan cewa, matakan Washington na tattalin arziki da kuma rufe mashigar Hormuz za su murƙushe tattalin arzikin Iran.

"Maƙaryaci, maƙaryaci, wando na ci da wuta," in ji Ghalibaf a cikin wani sako da ya wallafa a shafinsa na X a ranar Asabar, yana mai mayar da martani ga ikirarin Bessent cewa Washington ta kawo ganga miliyan 130 na mai zuwa kasuwa a cikin kwanaki 14 da suka wuce.

Rumbun Labarai
Shugaban Siriya ya naɗa tsohon shugaban ƙungiyar SDF/YPG a matsayin mai ba shi shawara
Babbar ɗimuwar Netanyahu: Mafarkin Turkiyya na shirin kai hari
Shugaban Iran ya yi kira ga ƙasashen Musulmai su daina bari ana kai hare-hare daga cikin ƙasashensu
Hare-haren Iran sun ragargaza cibiyoyin leken asirin Amurka a Gabas ta Tsakiya: Rahoto
Iran ta yi gargaɗin cewa yaƙi da Amurka nan gaba zai iya shafar duka shiyyar da ma fannin makamashi
Trump ya ce an cire abubuwan fashewa daga Mashigar Hormuz, ya gargaɗi Iran kan dasa wasu
Saudiyya da Faransa sun goyi bayan kafa ƙasar Falasɗinu, sun buƙaci Isra’ila ta janye daga Lebanon
Hantarar da Amurka ke yi mana za ta ta'azzara ƙoƙarin diflomasiyya, in ji Iran
Iran ta ci gaba da nuna rashin tsoro yayin da Amurka ke ci gaba da ƙara mata matsin lamba
Ya kamata yaƙi da Amurka ya ƙare yayin da Tehran ke da  'iko da mutunci': Pezeshkian
Sabbin takunkuman da Amurka ta saka mana ta'addanci ne a fannin tattalin arziki, in ji Iran
Tsohon Ministan Tsaron Isra'ila Yaalon ya zargi Netanyahu da neman rikici da Turkiyya
Ko dabarun yaƙi na Iran za su sanya Amurka sake tunani?
Iran na duba yiwuwar kai hari kan cibiyoyin sojin Amurka da ke Turai: Rahoto
Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa ta dakatar da kasuwanci da Iran har 'sai abin da hali ya yi'
Saudiyya ta yaba wa sabon ƙawancen tsaron teku da ya fara aiki
Iran ta ce ta yi nasara a 'yaƙi da kuma diflomasiyya' bayan Trump ya nemi a yi saranda
Trump ya yi barazanar kai wa Oman harin bam idan ta 'kawo cikas' a tattaunawar Amurka da Iran
'Ba za a iya ƙwace Hormuz ta saƙon X ko jirgin dakon jiragen yaƙi ko jawabin zaɓe ba' — Iran
Amurka da Iran sun amince su tsawaita wa'adin yarjejeniyar tsagaita wuta, in ji majiyoyin Pakistan