| Hausa
AFIRKA
2 minti karatu
Ɗaruruwan mayaƙan RSF ciki har da kwamandoji sun sauya sheka zuwa Rundunar Sojin Sudan
Rundunar Sojin Sudan ta ce ɗaruruwan mambobin RSF, ciki har da kwamandoji, sun sauya sheka daga mayaƙan ƙungiyar tare da shiga sahun sojojin hukuma.
Ɗaruruwan mayaƙan RSF ciki har da kwamandoji sun sauya sheka zuwa Rundunar Sojin Sudan
daruruwan mayakan RSF sun shiga rundunar sojin Sudan, in ji rundunar sojin a ranar 19, ga Agusta 2026

Rundunar Sojin Sudan ta ce ɗaruruwan mambobin Rundunar Sojin Sa-Kai (RSF), ciki har da kwamandoji, sun fice daga ƙungiyar, inda suka shiga cikin rundunar.

A cikin wata sanarwa da aka fitar a daren Talata, yankin Al Dabba (wanda ke cikin Jihar Arewacin Sudan), ya ambato kwamandan masu tsaron kan iyaka Mohamed Saleh Younes, yana sanar da sauya shekar wani babban rukunin mambobin RSF da kuma shawarar da suka yanke ta shiga rundunar sojin Sudan.

A cewar sanarwar, ƙungiyar ta ƙunshi mayaka 318 - ciki har da kwamandoji hudu - da kuma motocin yaƙi har guda 50.

An rawaito Younes na cewa, "Kofofin ƙasar a buɗe suke ga duk wanda ke son komawa cikin rundunar sojojin."

‘Haɗin kan Sudan’

Ya ƙara da cewa sojojin Sudan za su ci gaba da ƙoƙarinsu na dawo da tsaro a faɗin ƙasar.

Sanarwar ta kuma ambato Laftanar Kanar Musa Ali Ahmed, shugaban ƙungiyar da aka rawaito tana ɗauke da wannan rahoto, wanda ya danganta shawarar ƙungiyar da "rashin tsarin gudanarwa" a cikin RSF.

An ƙara ambaton Ahmed yana cewa jama’ar ta yanke shawarar shiga rundunar soji don "haɗin kan Sudan."

A makon da ya gabata, hukumomin Sudan sun sanar da cewa wasu mayaƙa 300, ciki har da kwamandoji 21, sun fice daga RSF kuma sun shiga rundunar sojin Sudan.

Mummunan yaƙi

Rundunar sojojin sa-kai ta RSF ta fuskanci ƙaruwar waɗanda suka sauya shekar mayaƙanta da shugabannin siyasa, musamman ma Mai ba ta Shawara kan Harkokin Siyasa Fares Al Nour, Kwamandan Rundunar Ali Rizqallah, da Manjo Janar Al Nour Ahmed Adam.

Tun daga watan Oktoban da ya gabata, jihohin Darfur da Blue Nile na Sudan - tare da Arewa, da Yammaci da Kudancin Kordofan - sun fuskanci mummunan fadace-fadace tsakanin sojojin Sudan da mayaƙan RSF.

Tun watan Afrilun 2023, Sudan na ci gaba da kasancewa cikin yaƙi tsakanin sojoji da rundunar sa-kai ta RSF.

A cewar ƙiyasin Majalisar Dinkin Duniya da na ƙasa da ƙasa, rikicin ya yi sanadiyyar mutuwar dubban mutane tare da raba kusan mutane miliyan 13 da matsugunansu.