| Hausa
AFIRKA
1 minti karatu
An kama ‘yar jarida mai yawan mabiya Denise Dusauchoy ‘yar kasar Kongo a Tanzania
Mahukuntan Kongo sun nuna cewa matakin wani bangare ne na binciken aikata muggan laifuka da dama da ake ci gaba da yi, kuma ba wai an ce tana da laifi ba ne.
An kama ‘yar jarida mai yawan mabiya Denise Dusauchoy ‘yar kasar Kongo a Tanzania
An kama Denise Dusauchoy karshen mako.

An kama 'yar jarida kuma mai yawan mabiya a Kongo Denise Dusauchoy a karshen mako a Tanzania bisa bukatar hukumomi a Jamhuriyar Dimokuradiyyar Kongo.

A cikin wata sanarwa da ta fitar a ranar Litinin, ma'aikatar shari'a ta Kongo ta ce kamawar ta biyo bayan sammacin kamawa da wata kotu ta bayar a kasar. Kinshasa ta nuna cewa matakin wani bangare ne na binciken laifuka da ake gudanarwa kuma ba wai an ce tana da laifi ba ne.

Dusauchoy, wacce ke sukar gwamnatin Shugaba Félix Tshisekedi, ta bayyana goyon bayanta a fili ga AFC/M23, wata kungiyar 'yan tawaye da ke da iko da manyan yankuna a gabashin DRC, a wani rikici da ya hada kungiyar da sojojin Kongo.

A watan Disamban shekarar 2024, an yanke mata hukuncin daurin shekaru uku a gidan yari a Kinshasa saboda yada jita-jita, aikata jabu da kuma cin mutuncin jama'a.