Shugaba Bola Tinubu ya ƙaddamar da ayyukan Bankin Duniya uku da kimar kudinsu ya kai dala biliyan $3.05 domin ƙarfafa shirin kiyaye zamantakewa da ƙwarewar mutane da kuma tallafi ga al’ummomi masu rauni a faɗin ƙasar.
An shirya ayyukan ne da zummar tabbatar da cewa alkhairin sauye-sauyen sun kai ga mutane ta hanyar inganta rayuwa da kuma damar samun muhimman hidindimu.
A cikin wani muhimmin jawabin taro da ministan kuɗi, Taiwo Oyedele, ya gabatar a madadinsa, Shugaba Tinubu ya bayyana shirye-shiryen a matsayin muhimman ginshiƙai na manufar gwamnatinsa ta Renewed Hope Agenda, yana mai cewa “an tsara ayyukan ne domin tabbatar da cewa ribar sauyin da ake yi wa tattalin arziƙin ƙasar sun samar da ingantacciyar rayuwa ga ‘yan Nijeriya.”
Ya ce shirye-shiryen za su faɗaɗa tallafi ga ƙananan manoma da ƙananan da matsakaitun masana’antu da ƙarfafa cibiyoyin kiwon lafiya a matakin farko da inganta koyarwa na sharan fage a makarantin gwamnati da kuma tallafa wa malamai.
Za su kuma haɓaka fayyace gaskiya a aikin gwamnatin a matakin mazaɓu da kuma samar da ababen more rayuwa da hanyoyinsa samun kuɗaɗen biyan buƙatu da kuma muhimman hididimu ga ‘yan gudun hijira da al’ummomin da ke karɓar baƙuncinsu.
Shugaban ya bayyana cewa ayyukan sun kasance tsari na ƙasa na rage talauci da inganta uwar kuɗi da ƙwarewar mutane da kuma juriyar mutane.
Ya jaddada cewa gwamnatin ta jajirce wajen tabbatar da cewa farfaɗowar tattalin arzikin ya kai ga ko wane iyali.
Bugu da ƙari, Shugaba Tinubu ya ce ; “Gyare-gyaren tattalin arzikin Nijeriya sun riga sun fara samar da sakamako na gari, inda kimar tattalin arziƙi a ma’aunin GDP ya ƙaru da kashi 11.2 cikin 100 da kuma ƙarin kudin shiga na kusan kashi 10 cikin 100 na dalar Amurka a cikin shekarar da ta gabata, yayin da ajiyar kudin Nijeriya a ƙetare ta zarce dala biliyan $50 yayin da hawhawar farashi ya ragu sosai daga ƙololuwar da ta kai a shekarar 2024.”
Ya kuma bayyana cewa gwamnatin ta faɗaɗa shirin raba tallafin kuɗi zuwa iyalai masu rauni miliyan 15, inda ta fitar da kimanin ‘yan Nijeriya miliyan 7.5 daga talauci.
Shugaban ya bayyana cewa shirye-shiryen sun dace da manufofin ci-gaban na gwamnatin shugaban, waɗanda suka mayar da hankali a kan faɗaɗa hanyoyin samun kuɗi ga tattalin arziki da ƙarfafa gwamnatoci a matakan ƙasa da gwamnatin tarayya a wani ɓangare na burin gwamnatin na gina tattalin arziki mai kimar dala tirliyan 1 nan da shekarar 2030.
Shugaban na Nijeriya ya yi kira a gwamnatocin jihohi da ƙananan hukumomi da abokanan aiki na harkar ci-gaba da kuma aiwatar da shirye-shiryen yadda ya dace, yan amai cewa nasararsu ya dangane da kan haɗin kai mai girma a dukkan ɓangarotin gwamnati.

















