| Hausa
NIJERIYA
2 minti karatu
INEC za ta yi zaɓen gwaji na Shugaban Ƙasa gabannin zaɓen 2027 na Nijeriya
Ya yi kira da a haɗa fasahar zaɓe da ta sadarwa a wuri ɗaya gabannin zaɓen 2027, yana mai gargaɗin cewa labaran ƙarya da aka kitsa da ƙirƙirarriyar basira na gagarumar barazana ga sahihancin zaɓukan.
INEC za ta yi zaɓen gwaji na Shugaban Ƙasa gabannin zaɓen 2027 na Nijeriya
Tsohon Hoto: A watan Janairu na shekarar 2027 ne za a yi zaɓen NijeriyaNigeria's presidential election, in Yola

Hukumar zaɓe mai zaman kanta ta Nijeriya, INEC tana tunanin aiwatar da zaɓen gwaji na Shugaban Kasa gabanin zabukan shekarar 2027, domin gwada tsarin tantance masu zaɓe da tura tare da duba sakamakon zaɓe a cikin wani yanayi da ya dace da na ranar zaɓe.

Shugaban INEC, Farfesa Joash Amupitan ne ya yi wannan bayani ranar Laraba a Abuja yayin da yake magana a taron ƙasa da ƙasa na ƙungiyar masana ilimin sadarwa da ƙwararru (ACSPN).

Amupitan, wanda wani kwamishina na hukumar Sani Adam ya gabatar da bayaninsa a taron, ya ce sahihancin tsarin zaɓen ba ya dogara ga na’urar BVAS da kuma takardun sakamako, har ma da yadda ‘yan Nijeriya suka gane da kuma yarda da bayanai game tsarin zaɓen.

Ya yi kira da a haɗa fasahar zaɓe da ta sadarwa a wuri ɗaya gabannin zaɓen 2027, yana mai gargaɗin cewa labaran ƙarya da aka kitsa da ƙirƙirarriyar basira na gagarumar barazana ga sahihancin zaɓukan.

Game da ƙarin yadda ake amfani da ƙirƙirarriyar basira wajen juya bayanai, shugaban na INEC ya ce amfani da fasahara ƙirƙrarriyar basira wajen juya bayanai ta hanyar ƙirƙiro bidiyo na ƙarya da murya ta ƙarya da hotuna sun ƙara zama masu araha kuma da wahalar ganowa.

Ya yi ishara ga yadda aka yaɗa bayanan ƙarya a zaɓukan da aka yi kwanan nan a yammaci da gabashin Afirka, ciki har da bayanai na ƙarya da ke da alaƙa da zaɓen 2023 na Nijeriya.

Amupitan ya yi gargaɗin cewa irin waɗannan ayyukan za su iya kai ga miliyoyin masu amfani da kafafan sada zumunta kafin masu bin diddigi su tabbatar da gaskiyar lamarin.

Ya ce barazanar ta wuce ƙirƙiro ƙarya kawai, yana mai cewa murɗa yadda kafafan ke aiki ta yadda za a rinƙa tura wa masu zaɓe saƙonni da ke karo da juna ba tare da wani dalili ba.

 

Rumbun Labarai
EFCC ta kori ma’aikatanta fiye da 40 saboda zargin cin hanci da rashawa a Nijeriya
Tinubu ya jinjina wa jami’an tsaron Nijeriya kan ceto masu yi wa kasa hidima da aka yi garkuwa da su
Gwamnatin Kano tana bukatar rigakafin cutar mashaƙo miliyan tara daga gwamnatin tarayya
Nijeriya ta nuna damuwa kan abin da ya faru a makwabciyarta Nijar
Shugaba Tinubu zai tafi Turai don fara hutun makonni uku
Babban Sufeton ‘Yansandan Nijeriya ya matsa ƙaimi don ceto waɗanda aka sace a masallacin Jihar Neja
'Yansandan Nijeriya sun kama likitoci kan zargin safarar mutane da cire musu ƙoda
Amurka na shirin janye sojojinta 200 da ta tura Nijeriya
Gwamnatin Nijeriya ta gargaɗi al’ummomi 915 a jihohi 19 kan barazanar ambaliyar ruwa
Sufeta Janar na ’Yansandan Nijeriya ya tura AIG zuwa jihar Neja don ceto masallatan da aka sace
EFCC za ta ba da ladan kashi 5 cikin 100 ga wanda ya ba da bayanai kan kadarorin sata da ke ƙetare
Hedikwatar tsaron Nijeriya ta tattauna da jakadan Saudiyya kan ƙarfafa alaƙar tsaro
Masu garkuwa da mutane a Nijeriya sun tara naira biliyan 7 na kuɗin fansa: Bincike
Ranar Hausa ta Duniya: Harshen Hausa ya gawurta, in ji Shugaba Tinubu
Shaguna aƙalla 300 sun ƙone a gobarar da ta tashi a  kasuwar Oranyan da ke Ibadan a Nijeriya
Dawo da tallafin fetur zai mayar da Nijeriya baya a cigaban tattalin arzikinta — Minista
Wani bidiyo ya nuna mutum 600 da aka yi garkuwa da su a wani harin masallaci a jihar Neja a Nijeriya
NDLEA ta kama wata tsohuwa mai shekara 101 da tabar wiwi a cikin garin alabo
Dakarun Nijeriya sun kashe fiye da 'yanta'adda 20 a samamen da suka kai Borno
Za mu tabbatar Tinubu ya lashe zaɓen Nijeriya na 2027— Abdulaziz Yari