A cikin littafinsa mai suna Al Muqaddimah (Gabatarwa), masanin tarihin Larabawa na ƙarni na 14, Ibn Khaldun, ya gabatar da ra'ayoyi waɗanda har yanzu suna tasiri ga tunanin siyasa, kamar Asabiyyah, wanda ke nufin haɗin kai na ƙungiya wanda ya samo asali daga gamayya.
Daga cikinsu akwai ra’ayinsa da ke cewa yanayin ƙasa da yanayi, tare da haɗin kai na zamantakewa, suna taka muhimmiyar rawa wajen tsara ci-gaban siyasa da rikicin soja.
Fiye da ƙarni shida bayan mutuwarsa, masana sun ce ra'ayoyin Ibn Khaldun sun kasance masu muhimmanci ga rikice-rikicen da ke faruwa a Mashigar Teku ta Hormuz tsakanin Amurka da Iran.
Duk da rashin daidaiton soja tsakanin ƙasashen biyu, Tehran ta yi amfani da matsayinta na ƙasa don ƙalubalantar Washington ta hanyoyin da suka yi daidai da ra’ayin masanin.
"A ƙarshe, tashin hankalin da ke kewaye da Mashigar Hormuz ya sake tabbatar da fahimtar Ibn Khaldun a zamanin yau: tarihi ba wai kawai yana tsara shi ta hanyar nufin shugabanni da girman rundunonin sojoji ba har ma da yanayin ƙasa da al'ummomi ke aiki a kai," in ji Kadir Canatan, masanin zamantakewa a Jami'ar Duzce kuma ƙwararre kan ayyukan Ibn Khaldun, a tattaunawarsa da TRT World.
Kodayake Amurka ta ci gaba da kasancewa babbar mai ƙarfi a fannin soja da tattalin arziki a duniya, gwamnatin Trump ta gamu da matsin lamba a yankin Tekun Fasha daga wata abokiyar gaba mai rauni.
Iran ta yi amfani da matsayinta na dabarun da ke kan Mashigar Teku ta Hormuz - daya daga cikin manyan wuraren da man fetur ke bi ya isa ga duniya - a matsayin matsin lamba ga tattalin arzikin Washington.
Ta hanyar kasancewar mashigar Hormuz mai nisan ‘yan kilomitoci kacal a mafi ƙanƙantarsa, na ɗauke da kusan kashi 20 zuwa 25 cikin 100 na cinikin mai na teku a duniya da kuma yawan iskar gas da ake buƙata a duniya.
Duk wani cikas da za a samu a wajen ya wuce batun fafatawar Amurka da Iran, yana da tasiri ga siyasar Gulf, kasuwannin makamashi na duniya da kuma tattalin arziki mai fadi.
"Da a ce Ibn Khaldun yana raye a yau, da zai ɗauki Hormuz a matsayin ɗaya daga cikin misalai mafi bayyana na zamani na sauyin yanayin ƙasa zuwa siyasa da tattalin arziki," in ji Canatan.
Yanayin kasa na iya taimakawa wajen daidaita bambance-bambancen da ke tsakanin karfin soja, ya danganta da inda rikici ya faru. Duk da cewa Amurka tana da karfin soja mai yawa, gabar tekun Iran da ke kusa da mashigar, tsibiran da ke kusa, sansanonin sojin ruwa, da karfin makamai masu linzami da jiragen sama marasa matuki suna ba ta babbar fa'ida a fannin dabarun yankin.
"Iran ba ta bukatar ta ci nasara a kan Rundunar Sojan Ruwa ta Amurka a yakin gaba da gaba; kawai sanya jiragen ruwa da yawa cikin hatsari, tayar da farashin ma'adinai, ko sauya lissafin hatsarin kamfanonin inshora ya isa ya rage cinikin duniya," in ji Canatan.
Ya ƙara da cewa, ƙananan hanyoyin ruwa kamar mashigar Hormuz na ba wa manyan kasashen yankin kamar Iran iko da damar yin amfani da ƙarfin iko na duniya.
Yanayin ƙasa na iya sauya ayyuka?
Duk da cewa ƙasashen Gulf kamar Saudiyya da Hadaddiyar Daular Larabawa suna neman hanyoyin fitar da mai, irin waɗannan ƙoƙarin za su ɗauki lokaci. Fiye da kashi 80 cikin 100 na cinikin duniya ana jigilar su ne ta teku.
Sakamakon haka, dakatar da ɗaya daga cikin waɗannan mawuyacin hali ko da na ɗan gajeren lokaci na iya haifar da "tashin hankali na tattalin arziki", Alex Mills, ƙwararren masanin ciniki na ƙasa da ƙasa, ya rubuta a watan Maris.
"Rufewa na dogon lokaci zai iya haifar da ci gaba da rikice-rikice a duniya cikin sauƙi, da kuma babban rikici a mafi munin yanayi.
"Iran ta nuna yadda ƙasa mai matsayi mai muhimmanci za ta iya haifar da girgizar tattalin arzikin duniya cikin sauƙi." in ji shi.
"Sakamakon zai iya zama mafi muni idan aka yi amfani da irin wannan ƙarfin a hannun wata ƙasa mai tattalin arziki mai ɗorewa ko kuma rundunar sojojin ruwa ta zamani," in ji shi, yana mai nuni da raunin kuɗin Iran da kuma raunin sojojin ruwan ƙasar, waɗanda yawancin jiragen ruwan yaƙinsu suka nutse sakamakon hare-haren haɗin gwiwa tsakanin Amurka da Isra'ila.
Duk da yadda Mills ya jaddada muhimmancin yanayin ƙasa bayan rikicin Iran da Amurka, ƙwararru sun yi gargaɗi game da rage ra’ayin Ibn Khaldun zuwa ga kalmar da aka fi sani da "yankin ƙasa ƙaddara ce."
Ko da yake galibi ana danganta kalmar "yankin ƙasa ƙaddara ce" ga Ibn Khaldun, ƙwararru sun ce bai taɓa amfani da waɗannan kalmomin a cikin rubuce-rubucensa ba.
Canatan kuma ya yi gargaɗi game da ɗaukar yanayin ƙasa a matsayin ƙaddara. Ya ce Ibn Khaldun ya ɗauki yanayin ƙasa a matsayin ɓangare ɗaya kawai na tsarin da ya faɗaɗa wanda ya haɗa da yanayin asabiyyah, ko haɗin kan jama'a.
"Idan aka yi amfani da tunanin Ibn Khaldun, yanayin ƙasa mai kyau zai iya canzawa zuwa iko mai ɗorewa ne kawai idan aka haɗa shi da ƙarfin asabiyyah (haɗin kai na zamantakewa), tsarin mulki (ikon mallaka/tsarin ƙasa), da isassun albarkatu kasa da na tattalin arziki," in ji shi.
Ko da yake Iran ta nuna juriya a rikicin Amurka da Isra'ila, Tehran ta ci gaba da fuskantar manyan rauni, ciki har da matsalolin tattalin arziki, ware ta a siyasa da rashin gamsuwa a cikin gida, wanda hakan ya sa ba a san tabbas game da yanayin rikicin na dogon lokaci ba.
Tahsin Gorgun, masanin tunanin Musulunci a Jami'ar Istanbul 29 ga Mayu, shi ma yana ganin kamanceceniya tsakanin ra'ayoyin Ibn Khaldun da rikicin Hormuz na yanzu.
Kamar Canatan, ya ce Ibn Khaldun bai ɗauki yanayin ƙasa a matsayin abin da ke ƙayyade al'amuran siyasa kawai ba, amma ya kuma yi la'akari da shi tare da yanayi da nau’in ƙasa.
Duk da haka, Gorgun ya yi imanin cewa karfin binciken ilimi na Ibn Khaldun kan yanayin ƙasa, yana taimakawa wajen bayyana rashin daidaiton da ke tsakanin mashigar ruwa ta Hormuz.
"Duk da cewa kowace ƙasa (Amurka da Isra'ila) tana da ƙarfin soja, tana iya fuskantar iyaka idan ta fuskanci wani cikas na ƙasa kamar mashigar Hormuz," in ji Gorgun a tattaunawar sa da TRT World.
A lokacin Yaƙin Cacar Baki, makamai masu linzami masu dogon zango sun rage kima muhimmancin ƙasa.
Amma tun bayan rugujewar Tarayyar Soviet, ƙasa ta sake yin fice a tsakanin tashin hankali a yankuna kamar na Balkans da Caucasus, in ji Mehmet Akif Kayapinar, farfesa a Cibiyar Nazarin Musulunci ta Jami'ar Istanbul.
Ya nuna ƙaruwar wallafe-wallafe kan wannan batu, ciki har da littafin Robert Kaplan mai suna ‘The Revenge of Geography’, a matsayin shaidar sake sha'awar tasirin ƙasa a siyasar duniya.
Duk da haka, Kayapinar bai gamsu da cewa za a iya amfani da ra'ayoyin Ibn Khaldun kai tsaye ga rikicin Hormuz na yanzu ba.
"Binciken nasa yana da nufin fassara cigaban siyasa na dogon lokaci maimakon abubuwan da suka faru na ɗan gajeren lokaci kamar rikicin Hormuz na yanzu," in ji Kayapinar ya yayin da yake tattauna da TRT World.
Yanayin kasar yankin Gulf ma na da muhimmanci
Yanayin ƙasa ya kuma tsara dangantaka mai sarkakiya tsakanin Iran wacce ta fi rinjayen Shi'a da maƙwabtanta Larabawa da Sunni ke jagoranta a faɗin Tekun Gulf.
Ƙasashen yankin Gulf masu arzikin mai da iskar gas—ciki har da Kuwait, Qatar, Bahrain, UAE da Oman—suna tsaye kai tsaye a faɗin Tekun daga Iran, suna ƙirƙirar wata alaƙa ta ƙasa da ba za a iya rabuwa da ita ba da Tehran.
Kodayake ƙasashen Gulf da yawa suna dauke da sansanonin sojojin Amurka kuma suna da alaƙa ta kud da kud da Washington, sun kuma nemi kiyaye dangantakar aiki da Iran, suna taimakawa wajen ci gaba da kasuwanci ta mashigar Hormuz ba tare da katsewa ba har zuwa lokacin da rikicin ya ci gaba da afkuwa.
"Kusanci a yanki yana tilasta nau'ikan dangantaka daban-daban. Har ma da ƙiyayya tana da iyaka. Saboda haka, idan ɓangarorin suka yi tunani game da wannan kusancin, za su iya yanke hukuncin cewa rayuwa cikin zaman lafiya da jituwa ita ce hanya mafi kyau ga kowa," in ji Gorgun, yana mai nuni da rikicin Iran da Gulf.
Gorgun kuma yana ganin kamanceceniya tsakanin ra'ayoyin Ibn Khaldun da kuma babban tashin hankali tsakanin Iran da ƙasashen Larabawa maƙwabta, gami da ƙasashe kamar Jordan waɗanda ke dauke da sojojin Amurka.
A cewar Gorgun, Iran ta haɓaka ƙaƙƙarfar fahimtar asabiyyanci ta hanyar asalin tarihin Farisa da al'adar siyasa ta Shi'a.
A akasin haka, ya bayyana cewa yawancin ƙasashen Gulf sun bullo ne daga shirye-shiryen siyasa na bayan Yaƙin Duniya na Farko waɗanda ƙasashen Yamma suka tsara, wanda ya ba su ƙarancin haɗin kai na zamantakewa.
Gorgun ya ce Ibn Khaldun ya yi muhawarar cewa ƙabilun Larabawa kafin Musulunci ba su da haɗin kai da ake buƙata don gina ƙasa mai ɗorewa har sai da suka haɗu kan saƙon Addini na Annabi Muhammadu.
Ta hanyar amfani da wannan tsari a yau, Gorgun ya yi muhawara da cewa wasu masarautun Gulf sun dogara sosai kan kawancen waje, wani abu da Ibn Khaldun ke gani a matsayin raunana 'yancin kai na siyasa.
A sabanin haka kuma, Gorgun ya ce matsayin Iran mai muhimmanci, tare da haɗin gwiwarta da Rasha da China, ya ƙarfafa matsayinta na siyasa.
"Ƙarfin da ya fahimci zurfin yanayinta kuma yana da ƙarfin tunanin asabiyyanci zai iya nuna ƙarfi fiye da ƙarfin da take da shi a zahiri," in ji shi, yana mai nuni da rikicin Iran da Amurka.
"Wannan wani abu ne da ke cikin ra’ayin Ibn Khaldun. Da yana raye a yau, da ya yi nazarin yanayin kamar haka," in ji Canatan.
"Fasahar soja mai girma ba za ta iya shawo kan asabiyyanci mai ƙarfi kai tsaye ba," in ji shi.
Amma ya kuma ƙara da cewa asabiyyanci kaɗai ba zai tabbatar da nasara ba.
"Za ta iya rushewa a ɗan kankanin lokaci idan ba a tallafa mata da ƙarfin cibiyoyi, albarkatun tattalin arziki, da kyakkyawan shugabanci ba," Canatan ya shaida wa TRT World, yana mai nuni ga raunin Iran.
"A ra’ayin Ibn Khaldun, tambayar da ke da muhimmanci ba ita ce wanne ɓangare ne ke da mafi ƙarfin makami ba, a'a, wanne ɓangare ne zai iya ci gaba da haɗin kai, ƙarfin kuɗi, haƙurin zamantakewa, da ƙawance na tsawon lokaci."



















