Mojisola Adeyeye ta bayyana cewa hukumar na aiki tare da ‘yan majalisa domin ganin haƙarsu ta cim ma ruwa.

Hukumar NAFDAC wadda ke kula da ingancin abinci da magunguna ta buƙaci a fara yanke hukuncin kisa ga waɗanda ke safarar jabun magunguna.

Daraktar hukumar Mojisola Adeyeye ce ta bayyana haka inda ta ce ya kamata a ɗauki wannan mataki musamman sakamakon yadda irin waɗannan magungunan ke jawo mutuwar yara, kamar yadda ta shaida wa gidan talabijin na Channels a ƙasar.

“Wani ya sayi magungunan yara kan N13,000, wani kuma yana sayar da shi N3,000 a cikin rukunin shaguna ɗaya,” kamar yadda shugabar ta NAFDAC ta bayyana a ranar Juma’a.

Shugabar ta NAFDAC ta bayyana cewa babu wasu sinadaren magance cuta da aka gani a cikin maganin bayan an gudanar da gwaji a kan maganin a ɗaya daga cikin ɗakunan gwajin na hukumar da ke Kaduna.

Hukumar ta NAFDAC ta bayyana cewa tana neman a samu goyon bayan ɓangaren shari’a domin su bayar da goyon baya kan hakan.

Ta bayyana cewa hukumar na aiki tare da ‘yan majalisa domin ganin haƙarsu ta cim ma ruwa.

TRT Afrika