| Hausa
TURKIYYA
2 minti karatu
Shugaba Erdogan ya yi kira kan a yi amfani da diflomasiyya yayin da rikicin Iran ke rincaɓewa
A yayin tattaunawa da Mohammed bin Salman na Saudiyya, Shugaba Erdogan ya yi gargaɗin cewa rashin dakatar da ƙaruwar hare-haren na iya haifar da “sakamako mai matuƙar muni” ga tsaron Gabas ta Tsakiya da duniya baki ɗaya.
Shugaba Erdogan ya yi kira kan a yi amfani da diflomasiyya yayin da rikicin Iran ke rincaɓewa
Erdogan ya mika saƙon fatan alheri bayan hare-haren da aka kai a baya-bayan nan kan Saudiyya / AA Archive
7 awanni baya

Recep Tayyip Erdogan ya yi wata tattaunawa ta waya da Mohammed bin Salman kan batun ƙaruwar tashin hankali a yankin Gabas ta Tsakiya bayan hare-haren da aka danganta da ƙaruwar rikicin da ya shafi Iran.

A cewar Hukumar Sadarwa ta Turkiyya a ranar Lahadi, Erdogan ya mika fatan alheri bayan hare-haren da aka kai a baya-bayan nan kan Saudiyya kuma ya yi gargaɗin cewa rashin dakatar da ƙaruwar hare-haren na iya haifar da “sakamako mai matuƙar muni” ga tsaron yankin da duniya baki ɗaya.

Kiran na zuwa ne yayin da Iran ke kai harin makamai masu linzami da jirage marasa matuƙa kan sansanonin sojin Amurka a kasashe da dama na Gabas Ta Tsakiya, inda ta ce tana kai hare-haren ne kan sansanonin da ake amfani da su wajen shirya hare-haren da ake kai mata. Ta kai hare-haren ramuwar gayyar kan ƙasashen Larabawa da dama tare da fargabar faɗaɗar yaƙin.

“Diflomasiyya ita ce hanyar da ta dace”

Ƙarin tashin hankali ya biyo bayan manyan hare-hare na haɗin gwiwa tsakanin Amurka da Isra'ila a cikin Iran da suka kai wa wuraren soja da wasu muhimman wurare, kuma rahotanni daga kafofin yada labarai na gwamnati na Iran da rahotannin ƙasa da ƙasa sun ce an kashe manyan shuwagabanni, ciki har da Jagoran Addinin Iran, Ali Khamenei.

A bisa wannan yanayi, Erdogan ya jaddada cewa Turkiyya da Saudiyya na iya ƙoƙarisu wajen ƙara tattaunawa, inda ya ƙara da cewa diflomasiyya ita ce hanyar da ta fi ma'ana don hana ɓarkewar rikici mafi girma.