| Hausa
TURKIYYA
3 minti karatu
Erdogan: Amincewar da Isra'ila ta yi wa Somaliland ba za ta amfani kowa ba
Ƙasashe a yankin dole su samar da mafita ga matsalolin yankin, a cewar Erdogan yayin taron manema labarai tare da Firayiministan Ethiopia Abiy a Addis Ababa.
Erdogan: Amincewar da Isra'ila ta yi wa Somaliland ba za ta amfani kowa ba
Shugaba Recep Tayyip Erdogan da Firaministan Habasha Abiy Ahmed sun halarci taron manema labarai na hadin gwiwa a Addis Ababa a ranar 17 ga Fabrairu, 2026. / AA
4 awanni baya

Shugaban Turkiyya Recep Tayyip Erdogan a ranar Talata ya taɓo batun matakin Isra’ila na amincewa da Somaliland a matsayin ƙasa mai ’yanci da ikon gudanar da kanta, kuma ta kasance ƙasa ɗaya tilo da ta yi hakan, yana mai jaddada cewa wannan mataki ba zai amfani Somaliya ko yankin ba.

“Ina so in sake jaddada cewa amincewar Isra’ila da Somaliland ba za ta amfani Somaliland ko Yankin Kusurwar Afirka ba,” in ji Erdogan a wata tattaunawa da manema labarai tare da Firayiministan Ethiopia Abiy Ahmed a Addis Ababa.

Ankara na ganin cewa ya kamata kasashen yankin su samar da mafita ga matsalolin yankin, in ji Erdogan, yana kira ga ƙasashen Kusurwar Afirka da kada su bari a mayar da shi “fagen fafatawar ƙasashen waje.”

Yana mai jaddada dangantakar diflomasiyya tsakanin Turkiyya da Habasha, Erdogan ya ce abin alfahari ne cewa fiye da kamfanonin Turkiyya 200, da jarin da ya kai $2.5 biliyan, suna tallafa wa samar da ayyukan yi ga kusan mutane 20,000 a Habasha.

‘Neman damar zuwa teku’

A ɗaya hannun, Firiyiministan Habasha ya ce ya nemi goyon bayan Turkiyya wajen ƙoƙarin Addis Ababa na tabbatar da samun damar zuwa teku, yana bayyana wannan a matsayin batu mafi muhimmanci a tattaunawarsa da shugaban Turkiyya.

Abiy ya faɗa a taron na manema labarai cewa ya tattauna buƙatar Habasha ta samun “damar zuwa teku” tare da Shugaban Turkiyya, kuma ya yi maraba da irin tattaunawa mai ƙarfi da ma’ana kan wannan batu.

Habasha, wadda ta kasance ƙasa ba ta da teku tun bayan samun ’yancin Eritrea a 1993, ta taɓa bayyana samun tabbacin hanyar teku a matsayin muhimmin abin da ya shafi dabarun ƙasa.

Ziyarar Erdogan ta kasance ɗaya daga cikin muhimman ziyarori da ba a fiye ganin irin su ba da suka ƙunshi ministocin harkokin waje da tsaro na Türkiye, da sauransu, kuma ta zo ne yayin da ƙasashen biyu ke ƙoƙarin ƙarfafa dangantakar tattalin arziki da siyasa a lokacin da ake cikka shekaru 100 da alaƙa tsakanin ƙasashen wadda ta fara a 1926.

Shugabannin sun tattauna faɗaɗa huldar kasuwanci, inda jami’an Habasha suka ce dukkan ɓangarorin suna son ƙara ciniki tsakaninsu zuwa akalla $1 biliyan.

Abiy ya kuma ƙarfafa gwiwar ƙarin masu zuba jari na kamfanonin Turkiyya a Habasha, wadda tuni ke ɗauke da ɗaya daga cikin mafi yawan tarin kamfanonin Turkiyya a Afirka kudu da hamadar Sahara, musamman a masana’antu da gine‑gine.

Bangarorin biyu sun kuma tattauna haɗin gwiwa a matakin duniya, ciki har da tattaunawar sauyin yanayi da suka shafi COP31, wanda za a gudanar a Turkiyya a shekara mai zuwa, sannan a Ethiopia.

Rumbun Labarai
Matar Shugaban Turkiyya da Sarauniyar Jordan sun ƙara jaddada ƙawance a Istanbul
Turkiyya ta kama jami'an Mossad na Isra'ila biyu a Istanbul kan leƙen asiri
Shugaba Erdogan ya tuna da girgizar ƙasa, ya ce ‘Turkiyya ta cika alkawarinta‘ na sake gina gidaje
Turkiyya ta bunƙasa taimakon da ta ke ba Somaliya na sojojin sama da ƙasa don yaƙi da ta'addanci
Shugaban Turkiyya Erdogan ya gana da Yarima Mai Jiran Gado na Saudiyya Mohammed bin Salman a Riyadh
Shugaban Turkiyya zai ziyarci Saudiyya da Masar a cikin wannan makon
Fidan na Turkiyya ya gargaɗi Amurka kan kai wa Iran hari, ya ce Tehran a shirye take ta tattauna
Zaman lafiyar Iran na da muhimmanci ga tsaron yankin: Turkiyya
Turkiyya da Nijeriya sun ƙudiri aniyar kyautata alaƙar kasuwanci, zuba jari da tsaro
Erdogan da Trump sun tattauna kan Syria da Kwamitin Zaman Lafiya na Gaza
Turkiyya ta goyi bayan Nijeriya a yaƙi da ta'addanci yayin da Erdogan ya karbi baƙuncin Tinubu
Ziyarar Tinubu a Turkiyya: Muhimman abubuwa a tsarin dangatakar Nijeriya
Ministan Harkokin Wajen Turkiyya Fidan ya gana da takwaransa na Nijeriya Tuggar
Ministan Harkokin Wajen Turkiyya da takwaransa na Nijeriya za su gana kan cinikayya da tsaro
Ministan Harkokin Wajen Turkiyya Hidan ya yaba da "Kwamitin Zaman Lafiya" na Gaza
Turkiyya ta ɗauki dukkan yarjejeniyar zaman lafiyar Gaza da mahimmanci: Erdogan
Fidan na Turkiyya zai halarci bikin sa hannu na 'Hukumar Zaman Lafiya' ta Gaza a Switzerland
An tono makarantar Islamiyya mai shekara 900 yayin aikin sabunta birni a yankin Anatolia a Turkiyya
‘Syria ta ‘yan Syria ce’: Erdogan ya yaba da yarjejeniyar zaman lafiya ta Damascus
Filin Jirgin Sama na Istanbul ya zama na biyu mafi hada-hada a Turai a 2025: Erdogan