| Hausa
GABAS TA TSAKIYA
2 minti karatu
Iran ta zargi ƙasashen Larabawa biyar da hannu a hare-haren Amurka-Isra’ila, ta nemi a biya ta diyya
Jakadan Iran a Majalisar Dinkin Duniya ya yi ikirarin cewa Saudiyya, Hadaddiyar Daular Larabawa, Bahrain, Qatar da Jordan sun 'karya wajibcin d ake kawunansu' inda suka ba wa Amurka-Isra'ila damar kai wa Tehran hare-hare.
Iran ta zargi ƙasashen Larabawa biyar da hannu a hare-haren Amurka-Isra’ila, ta nemi a biya ta diyya
Jakadan Iran a MDD Amir-Saeid Iravani, ya yi bayani a wajen zaman Kwamitin Tsaro na Majalisar a birnin New York na Amurka a ranar 10 ga Maris din 2026 / Reuters Archive
6 awanni baya

Iran ta nemi diyya daga ƙasashen Larabawa biyar, ciki har da Saudiyya, Hadaddiyar Daular Larabawa, Bahrain, Qatar da Jordan, tana zargin su da hannu a hare-haren da Amurka da Isra'ila suka kai mata.

A cikin wata wasiƙa da ta aike wa Sakatare Janar na Majalisar Dinkin Duniya Antonio Guterres da Shugaban Kwamitin Tsaro na Majalisar Dinkin Duniya Jamal Fares Alrowaiei a ranar Litinin, Wakilin Iran na Majalisar Dinkin Duniya Amir Saeid Irvani ya yi ikirarin cewa waɗannan ƙasashen "sun karya wajibcin da ke kan ƙasashen duniya" ta hanyar ba da damar kai hare-haren Amurka da Isra'ila kan Iran.

Sakamakon haka, ya kamata a ɗora musu alhakin kuma su biya diyya ga asarar da Iran ta fuskanta a lokacin yaƙin.

Yaƙin yankin ya ta’azzara bayan da Amurka da Isra'ila suka ƙaddamar da hare-haren haɗin gwiwa kan Iran a ranar 28 ga Fabrairu.

Tehran ta ƙaddamar da hare-hare kan Isra'ila, Iraki, Jordan da ƙasashen Gulf waɗanda ke dauke da kadarorin sojojin Amurka kafin a sanar da tsagaita wuta na makonni biyu a makon da ya gabata.

Dubban mutane sun mutu, wasu dubunnai kuma sun ji rauni a duk faɗin yankin.

Wakilan Iran da Amurka sun kammala tattaunawa na tsawon sa'o'i 21 a Islamabad, Pakistan, da sanyin safiyar Lahadi, ba tare da cim ma matsaya ba.