30 ga Agusta: Nasarar da ta buɗe hanyar tasowar Turkiyya ta zamani
TURKIYYA
5 minti karatu
30 ga Agusta: Nasarar da ta buɗe hanyar tasowar Turkiyya ta zamaniYaƙin da ya tabbatar da 'yancin Turkiyya ya kuma ɗora ƙasar a kan hanyar tsayawa da ƙafarta, da cin gashin kai da kasancewa mai faɗa-a-ji- a yankin.
Nasarar da Turkiyya ta samu a shekarar 1922 ta kafa harsashin ƙarni guda na ikon mallakar ƙasa, dogaro da kai a fannin tsaro, da kuma ƙaruwar tasirinta a yankin.

Turkiyya tana murnar Ranar Nasararta ta 104, ranar da ake tunawa da yaƙin da ya sauya ƙasra wadda ake fuskantar mamaya da rarrabuwa zuwa ƙasar da ta hau kan hanyar samun 'yanci.

Ranar 30 ga watan Agusta ita ce ranar yaƙi mai muhimmanci a shekarar 1922 wanda ya dakatar da nausawar Girka a yammacin Anatolia kuma ya share fagen matakan ƙarshe na Yaƙin 'Yancin Kan Turkiyya, da janyewar sojojin mamaya, da kuma kafa Jamhuriyar Turkiyya.

Ranar Nasara tana cike da bukukuwa da abubuwan da suka faru a faɗin ƙasar, ciki har da tunawa da Mustafa Kemal Ataturk da kuma sojojin da suka fafata a yaƙin.

Ranar kuma tana nuna bikin Ranar Sojojin Turkiyya, tana haɗa nasarar tarihi da rawar da sojoji ke takawa a cikin labarin ƙasar.

Don fahimtar dalilin da ya sa ranar 30 ga watan Agusta ta kasance cikin asalin ƙasar Turkiyya, ya zama dole a duba bayan fagen fama kansa.

Hanyar zuwa Dumlupinar

Mamayar ta fara ne a tsakiyar ɓurɓushin Yaƙin Duniya na Ɗaya. Nasarar da aka samu a kan Daular Usmaniyya ta bar Istanbul a ƙarƙashin ikon Ƙawancen ƙasashen waje, yayin da waɗanda suka yi nasara a Yaƙin Duniya na Ɗaya, wanda aka fi sani da Kasashen Entente, suka mamaye manyan sassan Anatolia yayin da shirin raba daular da aka yi nasara a kanta ya fara aiki.

Lokacin da sojojin Girka suka sauka a Izmir a watan Mayu na 1919, tare da goyon bayan sojojin Entente, suka fara dannawa cikin ƙasar, tuni an riga an fara raba yankin yankunan Daular Usmaniyya.

Turjiyar da ta faro daga Anatolia ta ta'allaka ne a kan kin amincewa guda ɗaya: mutanen da suke zaune a yankin ne za su yanke hukunci kan makomarta, ba wakilai a manyan biranen Turai ba.

A cikin shekaru uku masu zuwa, wannan yunƙuri ya girma daga 'yan sa-kai da suke warwatse zuwa rundunar da za ta iya tilasta wa duk wani mataki.

A watan Agusta na 1922, sojojin Turkiyya sun shirya tsaf don kawo ƙarshen lamarin. Sun ƙaddamar da Babban Hari a ranar 26 ga Agusta, suka karya ikon Girka cikin sauri suka kama Afyonkarahisar washegari, yayin da sojojin Girka suka koma Dumlupinar.

A ranar 30 ga Agusta, sojojin Turkiyya sun kewaye kuma suka yi nasara a kan babbar rundunar sojoji a Dumlupinar, a cikin yaƙin da aka tunawa a matsayin Yaƙin Babban Kwamanda.

Sojojin Turkiyya sun matsa gabansu zuwa yamma, suka isa Izmir a ranar 9 ga Satumba suka sake ƙwace birnin da aka fara mamayar.

Daga fagen daga zuwa jamhuriya

Dumlupinar ta yanke hukunci ba wai kawai saboda ta karya wata rundunar sojoji ba.

Ta kawar da babban cikas na soja na ƙarshe tsakanin Ƙungiyar Ƙasa ta Turkiyya da ikon Anatolia, ta share hanyar yaƙin Mudanya a watan Oktoba, tattaunawar Lausanne da ta biyo baya, da kuma sanarwar kafa Jamhuriyar Turkiyya a shekarar 1923.

Wannan jerin ya sauya nasarar fagen daga zuwa tushe na siyasa da shari'a na sabuwar ƙasa.

Haka jami'an Turkiyya ke ci gaba da kallon mahimmancin ranar 30 ga Agusta.

Shugaban Turkiyya Recep Tayyip Erdogan ya bayyana ranar a matsayin tashin al'ummar ƙasar da kanta, tare da amsa gwagwarmayarta ta rayuwa kuma an tabbatar da 'yancin kanta.

Ranar tana wakiltar ƙasa da aka kafa a matsayin wadda ta kammala tana zaɓar sharuɗɗan tsira maimakon karɓar waɗanda aka ba ta.

Abin da ya sa ranar 30 ga Agusta take da muhimmanci har yanzu

Mamayar ta ƙare a shekarar 1922, amma tunanin da ta bari, cewa dole ne a tabbatar da ikon mallaka maimakon hasashe, ta daɗe tsawon ƙarni na gina ƙasar Turkiyya ta hanyoyin da suka wuce bikin.

Ƙasar da a da ta dogara sosai ga masu samar da makamanta na ƙasashen waje, yanzu tana samar da fiye da kashi 85 cikin 100 na kayan aikinta na soja, tun daga jiragen sama marasa matuƙa da jiragen ruwa zuwa sauran kayayyankin yaƙi, kuma fitar da kayan aikinta na tsaro da na sararin samaniya ya zarta dala biliyan 10 a shekarar 2025.

Waɗannan alƙaluma sun nuna matsayin Turkiyya a matsayin ta biyu mafi girman soja a ƙawancen NATO ta hanyar ma'aikata masu aiki da kuma rawar da take takawa a matsayin abokin hulɗar tsaro da masana'antu fiye da ƙungiyar.

Wannan rawar ta sake bayyana a wannan watan na Agusta, lokacin da Turkiyya ta sanya hannu kan yarjejeniyar tsaro ta haɗin gwiwa da Saudiyya da Pakistan da aka gina bisa ga haɗin gwiwa.

Yarjejeniyar ta sanya Ankara cikin tsarin tsaron yanki wanda take ƙara taimakawa wajen tsarawa maimakon mayar da martani kawai.

Babu ɗaya daga cikin waɗannan da ke cikin tunanin sojojin da suka yi yaƙi a Dumlupinar.

Suna fama da wata tambaya mai tsauri, ko Anatolia za ta ci gaba da kasancewa tasu kwata-kwata.

Duk da haka duk abin da ya biyo baya daga amsar da suka samu, tun daga Jamhuriyar kanta har zuwa tushen masana'antu da kuma isa ga dabarun da Turkiyya ta gina a cikin ƙarni na gaba, ya koma fagen fama a Kutahya a kwanakin ƙarshe na watan Agusta 1922.

A yau, 30 ga Agusta ta zama abin girmamawa ga ƙasar da ta ƙi miƙa wuyan makomarta.

Fiye da ƙarni ɗaya bayan haka, wannan nasarar ta kasance alama ce ta ƙudurin Turkiyya ta tsara makomarta.

Rumbun Labarai
Turkiyya ta ƙaddamar da shirin 2026–2030 na zama cibiyar fasahar AI ta duniya
Trump ya yi 'murna' kan yarjejeniyar tsaro ta Makka da Turkiyya da Pakistan da kuma Saudiyya suka yi
Shugaba Erdogan ya jinjina wa shekara 25 na Jam'iyyar AK kan samar da 'sauyi mai tarihi' a Turkiyya
Shekaru 25 na Jam’iyyar AK da matsayin Turkiyya na mai taka rawa a yanki da ma duniya
Ministan Harkokin Wajen Masar ya gode wa Turkiyya saboda tarban karamci da ta yi wa Mohamed Salah
Turkiyya ta yi kira ga Tunisia da ta saki jagoran Ennahda Ghannouchi da ke tsare a kurkuku
Turkiyya ta kama mutum 30 a wani samame da aka kai kan ƙungiyar masu aikata laifuka ta Alihan
Turkiyya za ta ci gaba da taka rawa da kuma shiga tsakani a Libya, in ji Ministan Harkokin Waje
Cikin hotuna: Turkiyya ta haskaka muhimman wurare don murnar Yajejeniyar Tsaron Hadin Gwiwa ta Makka
An fara gasar baje-kolin jiragen sama marasa matuka ta TEKONOFEST a garin Sirnak na Turkiyya
Erdogan zai kai ziyara Saudiyya don tattaunawa da Mohammed bin Salman da Firaministan Pakistan
Shugaban sadarwa na Turkiyya ya ce Isra'ila na yi wa yunƙurin zaman lafiya na Gaza zagon ƙasa
Turkiyya ta kama ɗanta'addan FETO da ake nema bisa yunƙurin kashe Shugaba Erdogan a shekarar 2016
Turkiyya ta yi fice a Gasar Duniya ta Rubutu a Kwamfuta da kambi 36
Turkiyya da Nijeriya sun ƙara ƙarfafa haɗin gwiwa kan ƙera jiragen ruwa
Shugaba Erdogan ya taya tawagar Sultans of Net ta Turkiyya murnar lashe gasar ƙwallon raga ta mata
Shugaba Erdogan ya yi taron cika shekaru shida da sake bude Hagia Sophia don Ibadar Musulmai
Ayyukan ‘yan kama-wuri-zauna na Isra’ila na barazana ga ƙoƙarin zaman lafiya a Ƙudus: Turkiyya
Turkiyya ta yi kira ga Amurka da Iran su koma kan yarjejeniya, su kuma yi aiki tare da Qatar
Girgizar ƙasa mai ƙarfin maki 5 ta auka wa gabashin Turkiyya