| Hausa
TURKIYYA
4 minti karatu
Turkiyya ba za ta bari a toshe hanyar ci-gabanta ba: Erdogan
Shugaban Turkiyya ya ce Ankara ba za ta tsaya ta zuba ido tana kallon ƙoƙarin yi wa ƙasar ƙawanya ba, a lokacin da ya yi alƙawarin bin hanyar salama da cim ma zaman lafiya da bunƙasar tattalin arziki.
Turkiyya ba za ta bari a toshe hanyar ci-gabanta ba: Erdogan
Shugaba Erdogan yana jawabi bayan taron majalisar ministoci a Ankara, Turkiyya, a ranar 7 ga Satumba, 2026.

Shugaban Turkiyya, Recep Tayyip Erdogan, ya yi gargaɗi game da matakan ƙiyayya da nufin yi wa Turkiyya ƙawanya, inda ya ce ƙasar ba za ta bari a toshe hanyarta a matsayin ƙasa mai 'yanci da bunƙasa ba.

“Kada kawaicinmu da kwanciyar hankalinmu su sa wani ya yi tunani yin rawar kai a wani wuri. A waɗannan ƙasashe da muka mayar da su gida ta hanyar bayar da rai da ɗaukan rai, ba za mu yarda wani ya gudanar da wani abu ba,” Erdogan ya faɗa a ranar Litinin bayan taron Majalisar Zartarwa a Fadar Shugaban Kasa a Ankara.

“Ba za mu zauna muna kallo daga gefe ga matakan ƙiyayya da nufin yi wa ƙasarmu ƙawanya a yankinmu ba. Turkiyya ba ta adawa da kowace ƙasa, al'umma, addini, ko al'ada,” in ji shi.

“Muna son ci gaba da tafiyarmu a matsayin ƙasa mai 'yanci da wadata a cikin wannan yanki mai wahala. Ba za mu taɓa yarda a toshe wannan hanya ba,” kamar yadda ya ƙara da bayyanawa.

“Waɗanda suka damu da yadda ƙasarmu take ƙara ƙarfi da kuma ƙoƙarinmu na samar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankinmu ba za su iya juyar da mu daga inda muka dosa ba.”

Haɗin kai da zumunci

“Mun dage wajen yin aiki domin tabbatar da cewa haɗin kai da ƙulla zumunci sun samu gindin zama a faɗin yankinmu mai girma, bisa ga manufarmu ta ƙawance da haɗin kai,” in ji Erdogan.

Dangane da kifewar jirgi a makon da ya gabata a gaɓar tekun garin Girne a Jamhuriyar Cyprus ta Arewa (TRNC), Erdogan ya ce: “Da haɗin gwiwa da TRNC, a halin yanzu muna tallafa wa bincike da jiragen ruwa guda tara da jiragen sama 11.”

“Za mu ci gaba da bunƙasa dangantakarmu da Kungiyar Haɗin Gwiwar Shanghai, wacce muke ganin tana tallafa wa ayyukan Majalisar Dinkin Duniya,” in ji Erdogan, yana magana bayan babban taron ƙungiyar a makon da ya gabata a Kyrgyzstan, inda ya halarta a matsayin baƙon ban-girma.

‘Ƙarya da tuggun' Isra'ila sun tarwatsa ƙoƙarin zaman lafiya”

Ta fuskar rikice-rikice a yankin, Erdogan ya zargi Isra'ila da haddasa yaƙi a Gabas ta Tsakiya da kuma mummunan tasirin da hakan ke da shi.

“Asarar da wannan yaƙi ya haifar da ya faro sakamakon ƙulle-ƙulle da tayar da zaune tsaye na Isra'ila ba su tsaya a kan 'yan Iran kaɗai ba, ba su tsaya a kan ƙasashen Gabas ta Tsakiya da muke da alaƙa da su kaɗai ba, har ma kowa, ko da yana da hannu ko ba shi da hannu,” in ji shi.

Ya kuma zargi Isra'ila da kawo cikas ga yarjejeniyar watan Yuni da nufin kawo ƙarshen yaƙin.

“Ƙarya da tuggun Isra'ila ne suka sa yarjejeniyar Islamabad, wacce ta kawo sauƙi ga dukan yankinmu, ta zama ba ta aiki,” in ji Erdogan.

Ci gaba da tafiyar tattalin arzikin Turkiyya

“Guguwar rikice-rikice a yankinmu ba za ta lafa ba har sai wannan ra'ayin mai tsanani, wanda ke kallon kowane ƙaramin yiwuwar zaman lafiya a matsayin barazana, ya canza,” in ji shugaban.

Duk da hayaniya da tashin hankali a yankin, Erdogan ya ce Turkiyya za ta ci gaba da tafiyar da tattalin arzikinta a hanyar bunƙasa da haɓaka.

“Ko da yake muna yin wasu gyare-gyare ga burukanmu, muna ci gaba da wanzar da tattalin arzikin Turkiyya a kan hanyar ci gaba da bunƙasa,” in ji shi.

“Za mu ci gaba da ɗaukar matakai da za su ƙara wadata ga al'ummarmu kuma su samar da mafita ta din-din-din ga matsalolin tsarin tattalin arzikinmu,” a cewar Erdogan.

“Za mu yi duk abin da ya zama dole don sa tattalin arzikin Turkiyya ya zama ƙarfi, mai goyayya, kuma mai juriya a kowane fanni,” in ji shi.

.