| Hausa
GABAS TA TSAKIYA
2 minti karatu
Iran ta yi gargaɗin cewa sabon harin Amurka da Isra'ila zai iya faɗaɗa rikici fiye da yankin
Rundunar kare juyin juya halin Iran (IRGC) ta ce Tehran ba ta gama amfani da dukkan ikonta kan abokan gaba ba tukunna.
Iran ta yi gargaɗin cewa sabon harin Amurka da Isra'ila zai iya faɗaɗa rikici fiye da yankin
Wani mutum na wucewa a gefen wani zanen ƙin jinin Isra'ila a Tehran, Iran. / AP / AP

Rundunar kare juyin juya halin Iran (IRGC) ta yi gargaɗi ranar Laraba cewa duk wani sabon hari na Amurka da Isra’ila zai iya janyo wani rikici mai faɗi da zai iya wuce yankin.

A wata sanarwar da kamfanin dillancin labaran Tasnim ya ɗauka, rundunar IRGC ta ce Amurka da Isra’ila sun gaza koyan darasi daga abin da ta bayyana a matsayin shan kaye na dabaru a-kai-a-kai daga hannun Iran.

Rundunar ta yi iƙirarin cewa duk da hare-haren da aka kai da “dukkan ikon soji biyun da suka fi tsada a duniya ,” Iran ba ta gama amfani da dukkan ikonta a kan abokan gaba ba .

“Idan aka ci gaba da maimaita tsangwama a kan Iran, yaƙin na yanki da aka yi alƙawarinsa a wannan karon zai bazu fiye da yankin,” in ji sanarwar.

Rundunar IRGC ta kuma yi gargaɗin “hare-hare na murƙushewa” a wuraren [da] “ba za ku iya zata ba.”

“Mu mazajen yaƙi ne, kuma za ku ga ƙarfinmu a fagen daga , ba wai a sanarwa na banza kawai ko kuma shafukan intanet ba,” in ji sanarwar.

Shugaban Donald Trump ya bayyana ranar Litinin cewa shi ya ɗaga kai hari kan Iran ne bisa buƙatar shugabannin ƙasashen Larabawa na gaɓar teku.

Pakistan ta ce tana aiki domin farfaɗo da tattaunawar diflomasiyar da ta ci tura tsakanin Iran da Amurka, biyo bayan wata yarjejeniyar tsagaita wuta da Pakistan ta samar ranar 8 ga watan Afrilu.

Amurka da Isra’ila sun ƙaddamar da hare-hare kan Iran ranar 28 ga watan Fabrairu, lamarin da ya janyo hare-haren ramuwar gayya daga Tehran a kan Isra’ila da kayayyakin Amurka a yankin , tare da rufe mashigin ruwan Hormuz.

Rumbun Labarai
Amurka ba ta bayar da wani rangwame mai gamsarwa ba a martaninta ga Iran: Kafofin watsa labaran Iran
Kotun Hukunta Manyan Laifuka ta Duniya ta bayar da umarnin sirri don kama jami'an Isra'ila biyar
Ben-Gvir ya sanar da shirin Isra'ila na gina sabbin haramtattun matsugunai a Lebanon
Har yanzu Amurka ba ta ba da bizar Gasar Kofin Duniya ga tawagar ƙwallon ƙafar ƙasarmu ba: Iran
Netanyahu na Isra'ila ya yi tattaunawar sirri a UAE da Al Nahyan yayin yaƙin Iran
Saudiyya ta kai hare-haren sirri kan Iran bayan an kai mata hari — Rahoto
Bayanan sirri na Amurka sun nuna cewa Iran na da iko da makamai masu linazami masu ƙarfi - Rahoto
Fidan ya yi gargadi kan amfani da Mashigar Teku ta Hormuz a matsayin makami a rikicin yankin
An jikkata sojojin Isra’ila takwas yayin kutse a Lebanon duk da yarjejeniyar tsagaita wuta
Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa ta riƙa kai hare-hare Iran a asirce a yaƙin Amurka da Isra'ila: rahoto
Rusassun cocina, alamomin Kiristanci da salon hare-haren Isra’ila da ke ci gaba a Lebanon
Trump ya kira martanin Iran ga shawarar zaman lafiya abin da 'ba za a lamunta ba kwata-kwata'
Iran ta mayar da martani ga masu shiga tsakani na Pakistan kan shawarar Amurka ta kawo ƙarshen yaƙi
Saudiyya ta musanta zargin bayar da izinin amfani da sararin samaniyarta don ayyukan soja
Iran ta harba makamai masu linzami ga sojin Amurka bayan hari kan tankar dakon manta
Darussa daga sabon tsarin tafiyar da duniya: Ba za a iya sayen tsaro ba, amma dole a gina shi
Trump ya dakatar da shirinsa na taimaka wa jiragen ruwa wucewa ta Mashigar Hormuz
Shugabannin duniya na matsa wa Iran lamba yayin da ake fargabar batun tsagaita wuta zai iya rushewa
Harin da Amurka ta kai Mashigar Hormuz ya kashe fararen-hula 5, a cewar Iran
Iran ta ce duk wani shirin Amurka kan mashigar Hormuz zai zama keta yarjejeniyar tsagaita wuta