Ɗanwasan gaba na ƙungiyar Manchester City, Antoine Semenyo, da kuma tsohon ɗanwasan tsakiyar Arsenal, Thomas Partey, suna cikin jerin sunayen 'yanwasan 26 da koci Carlos Queiroz ya zaɓa domin wakiltar Ghana a Gasar Kofin Duniya.
Tawagar ta Ghana za ta fafata da takwararta ta Wales a birnin Cardiff ranar Talata a wasan sada zumunta, kafin daga bisani su garzaya Arewacin Amurka domin halartar Gasar Kofin Duniya, wanda shi ne karo na biyar da ƙasar take halartar gasar.
Daga cikin 'yanwasan tsakiya akwai Partey mai shekaru 32 da ke buga wa Villarreal wasa, wanda ake sa ran zai gurfana gaban kotu a Birtaniya nan gaba kaɗan kan zargin fyaɗe da cin zarafin mata, ko da yake ya musanta laifin.
Tsohon ɗanwasan gaba na kungiyar Leicester City, Jordan Ayew, shi ne zai jagoranci ƙungiyar ta Black Stars a matsayin kyaftin, yayin da ɗanwasan gefe na Tottenham, Mohammed Kudus, ba zai samu damar buga gasar ba saboda rashin lafiya.
Semenyo mai shekaru 26 ya zura ƙwallaye 11 a wasanni 27 da ya buga wa City bayan ya koma can daga Bournemouth a watan Janairu kan kudi fam miliyan £62.5.
Za a fara Gasar Kofin Duniyar ne a ƙasashen Amurka, Canada, da kuma Mexico a ranar 11 ga watan Yuni, inda Ghana za ta fafata da Panama a wasanta na farko a rukunin L bayan kwanaki shida da fara wasan. Sauran ƙasashen da ke cikin rukunin da ake ganin za a fafata sun haɗa da Ingila da Croatia.
Jerin Sunayen 'Yan Wasan Ghana
Masu Tsaron Gida: Benjamin Asare, Lawrence Ati-Zigi da Joseph Anang.
‘Yan Baya: Baba Abdul Rahman, Gideon Mensah, Marvin Senaya, Alidu Seidu, Abdul Mumin, Jerome Opoku, Jonas Adjetey, Kojo Oppong Peprah da Derrick Luckassen.
'Yan Wasan Tsakiya: Elisha Owusu, Thomas Partey, Kwasi Sibo, Augustine Boakye, Caleb Yirenkyi, Abdul Fatawu, da Kamaldeen Sulemana.
'Yan Wasan Gaba: Christopher Bonsu Baah, Ernest Nuamah, Antoine Semenyo, Brandon Thomas-Asante, Prince Adu, Inaki Williams, da Jordan Ayew.







