"Kotun ta gano cewa ci gaba da kasancewar Isra'ila a yankin Falasdinawa da ta mamaye haramun ne," in ji Salam. / Hoto: AFP

Kotun hukunta manyan laifuka ta kasa da kasa (ICJ) a ranar Juma’a ta yanke hukuncin cewa yankunan Falasdinawa da aka mamaye sun zama “yanki daya,” wanda za a ba shi kariya da mutuntawa.

Da take jaddada cewa dokokin Hague sun zama wani bangare na dokokin kasa da kasa na al'ada, don haka suna aiki akan Isra'ila, kotun ta ce, "Kariyar da Yarjejeniyar Kare Hakkokin Dan'adam ke bayarwa ba ta gushewa idan ana rikici ko kuma mamaya."

Dangane da mamayar da Isra'ila ta yi wa yankunan Falasdinawa, kotun ta yi nuni da cewa, "cin gajiyar albarkatun kasa" da Isra'ila ke yi a yankin Falasdinu da ta mamaye, "ya saɓa da wajibcinta" na mutunta 'yancin Falasdinawa.

Musamman kan korar da aka yi a Gabashin Ƙudus da Yammacin Gaɓar Kogin Jordan, kotun ta jaddada cewa manufofin Isra'ila da ayyukanta sun saɓa wa yarjejeniyar Geneva ta 4 na haramcin miƙa mutanen da aka tsare ta tilas.

"Manufar sasantawa da Isra'ila ta saɓa wa yarjejeniyar Geneva ta 4," in ji ta.

Kotun ta ce manufofin Isra'ila da ayyukanta sun sa ta mamaye yankunan Falasdinawa, kuma ba ta da ƙwarin gwiwa cewa tsawaita dokar Isra'ila zuwa Gabar Yammacin Kogin Jordan da kuma Gabashin Birnin Ƙudus ya dace.

Kotun ta ICJ ta kuma ci gaba da cewa, Isra'ila ta sami damar yin amfani da muhimmin iko a kan Gaza duk da janyewar sojojinta a shekarar 2005.

'Dole a kawo ƙarshen mamayar Isra'ila'

Mamayar da Isra'ila ta kwashe shekaru da dama tana yi wa yankunan Falasdinawa haramun ce kuma ana bukatar kawo karshenta "cikin sauri kamar yadda zai yiwu", a cewar babbar kotun ta MDD a yau Juma'a.

"Kotun ta gano cewa ci gaba da zaman Isra'ila a yankin Falasdinu haramun ne," in ji alkalin kotun ICJ Nawaf Salam a ranar Juma'a, inda ya ƙara da cewa: "Dole ne Isra'ila ta kawo ƙarshen mamayar cikin hanzari."

"Kotun ta gano cewa ci gaba da kasancewar Isra'ila a yankin Falasdinawa da ta mamaye haramun ne," in ji Salam.

ICJ ta umurci Isra'ila da ta biya "cikakkiyar diyya", ga dukkan Falasdinawa kan duk wani "ba daidai ba" da ta yi musu a karkashin mamayar tun shekarar 1967.

Falasdinawa sun yi mruna da hukuncin kotun ICJ

Karamin Ministan Harkokin Wajen Falasdinu Varsen Aghabekian Shahin ya ce wannan "babbar rana ce ga Falasdinu" bayan da babbar kotun Majalisar Dinkin Duniya ta yanke hukuncin mamayar da Isra'ila ta yi na tsawon shekaru da dama da suka wuce ba bisa ka'ida ba.

"Wannan babbar rana ce ga Falasdinu, a tarihi da kuma bisa doka," kamar yadda ya shaida wa AFP, yayin da yake magana a madadin Ma'aikatar Harkokin Wajen Falasdinu.

"Wannan ita ce hukumar shari'a mafi girma a duniya kuma ta gabatar da cikakken nazari kan abubuwan da ke faruwa ta tsawon lokaci na mamayar da Isra'ila ke yi wa yankin Falasdinu wanda ya saɓa wa dokokin kasa da kasa."

TRT World