| Hausa
KASUWANCI
2 MINTI KARATU
Tinubu na son Majalisar Dokokin Nijeriya ta amince ya karbo bashin N1.77tn
Idan har majalisar ta amince, to za a yi amfani da bashin wajen cike giɓin kasafin kudin kasar na 2023 na naira tiriliyan 9.7.
Tinubu na son Majalisar Dokokin Nijeriya ta amince ya karbo bashin N1.77tn
Shugaban Majalisar Wakilai ne ya karanta buƙatar Shugaban Ƙasar a yayin zaman majalisar a ranar Talata. / Others
19 Nuwamba 2024

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu ya rubuta wa Majalisar Dokokin neman ta amince a karɓo bashin naira tiriliyan 1.767 a matsayin shirin dokar kasafin kudi na 2024 na sabon rancen da za a ciyo daga waje.

Idan har majalisar ta amince, to za a yi amfani da bashin wajen cike giɓin kasafin kudin kasar na 2023 na naira tiriliyan 9.7.

Shugaban Majalisar Wakilai ne ya karanta buƙatar Shugaban Ƙasar a yayin zaman majalisar a ranar Talata.

Shugaban Ƙasar ya kuma miƙa wa majalisar ƙudurorin samar da Shirin Bayar da Tallafi na Ƙasa da kuma na MTEF/ FSP 2025- 2027, don aiwatar da shirye-shiryen gwamnatin tarayya na tallafa wa mutane.

Wannnan na zuwa ne a yayin da Babban Bankin Nijeriya CBN a kwanan nan ya ce Gwamnatin Tarayya ta kashe dala biliyan 3.58 don biyan bashin ƙasashen waje da ake bin ƙasar a watanni taran farko na shekarar 2024.

MAJIYA:TRT Afrika