| Hausa
KASUWANCI
2 MINTI KARATU
Saudiyya za ta ƙulla yarjejeniyar dala miliyan 500 da ƙasashen Afirka
Ministan Kuɗi na ƙasar Mohammed Al-Jadaan ne ya bayyana hakan a ranar Alhamis, yayin wani Taron Tattalin Arziki na Saudiyya da Ƙasashen Afirka da ake gudanarwa a birnin Riyadh.
Saudiyya za ta ƙulla yarjejeniyar dala miliyan 500 da ƙasashen Afirka
“Muna aiki da abokan hulɗarmu don tallafa wa Ghana da sauran ƙasashe kan batun basussukansu,” Jaddan ya ƙara da cewa. Hoto: Reuters / Others
9 Nuwamba 2023

Asusun Ayyukan Cigaba na Saudiyya zai sanya hannu kan wasu yarjeniyoyi na riyal biliyan biyu, kwatankwacin dala miliyan 533 da ƙasashen Afirka.

Ministan Kuɗi na ƙasar Mohammed Al-Jadaan ne ya bayyana hakan a ranar Alhamis, yayin wani Taron Tattalin Arziki na Saudiyya da Ƙasashen Afirka da ake gudanarwa a birnin Riyadh.

“Muna aiki da abokan hulɗarmu don tallafa wa Ghana da sauran ƙasashe kan batun basussukansu,” Jaddan ya ƙara da cewa.

Tun da fari a wajen taron, Ministan Zuba Jari na Saudiyya Khalid Al-Falih ya ce arzikin fiye da dala biliyan 700 da ke asusun na Saudiyya, zai yi tasiri matuƙa wajen “kawo sauyi na ban mamaki” a fannin zuba jari a Afirka.

Ministan Makamashi Yarima Abdulaziz bin Salman, shi ma a wajen taron ya sanya hannu kan wasu yarjejeniyoyi na farko da ƙasashen Afirka ciki har da Nijeriya da Senegal da Chadi da kuma Habasha don haɗin kai a abubuwan da suka shafi makamashi.

MAJIYA:Reuters