| Hausa
AFIRKA
2 MINTI KARATU
'Yan bindiga sun kashe 'yan bijilanti 21 a Katsina
Rundunar 'yan sandan Nijeriya ta ce 'yan bindigan sun kai hari ne ga 'yan bijilantin a lokacin da suke dawowa daga wurin ta'aziyyar wani ɗan ƙungiyar bijilanti ta Katsina State Community Watch Corps da ya rasu.
'Yan bindiga sun kashe 'yan bijilanti 21 a Katsina
Sai dai ta wani ɓangaren kuma wasu daga cikin jama’ar yankin na cewa mutanen da suka rasu sun kai 30. / Others
10 Janairu 2025

Rundunar ‘yan sandan Nijeriya ta ce ‘yan bindiga sun kashe ‘yan bijilanti 21 a jihar.

Lamarin ya faru ne a ranar Talata a ƙauyen Baure da ke Ƙaramar Hukumar Safana yayin da ‘yan bijilantin ke dawowa daga wurin ta’aziyyar wani ɗan ƙungiyar bijilanti ta jihar da ya rasu.

Rundunar ‘yan sandan ta ce tun bayan samun rahoton lamarin, jami’ansu suka garzaya wurin inda suka kai ɗauki da kuma tabbatar da komai ya lafa.

Rundunar ‘yan sandan ta ce wasu ‘yan bindiga ne waɗanda suka shahara a yankin na Safana suka kai hari kan ‘yan bijilantin.

Sai dai ta wani ɓangaren kuma wasu daga cikin jama’ar yankin na cewa mutanen da suka rasu sun kai 30.

Haka kuma rahotanni sun ce ‘yan bindigar sun ƙona wasu gawawwakin sannan kuma ba a ga wasu ba.

MAJIYA:TRT Afrika da abokan hulda
Rumbun Labarai
Sudan: Aƙalla mutum 21 sun mutu a hatsarin kwale-kwale a Kogin Nilu
Kasashe shida sun shiga Kwamitin Tsaro na Tarayyar Afirka
RSF ta kashe ƙananan yara a harin da ta kai wani masallaci a yankin Kordofan na Sudan
Saudiyya ta yi tur da RSF kan munanan ayyukanta a Al Fasher, ta buƙaci a ba da hanyar kai agaji
Mutum biyar sun mutu a hatsarin helikwaftan ɗaukar marasa lafiya a Libya
Yadda 'yan Somaliya suka gina wa tsohon shugaba ƙasarsu Farmaajo sabon gida
Sake dawo da ainihin martabar Afirka
RSF ta Sudan ta kai hari da jirgi maras matuƙi, ta kashe gomman mutane da yara
Dubban ‘yan kasar Libya sun taru don halartar jana'izar Saif al-Islam Gaddafi
Harin RSF a wani asibiti a Sudan ya kashe mutum 22, ciki har da ma'aikatan jinya
Ghana da Zambia sun ƙulla yarjejeniyar shiga ƙasashen juna ba tare da biza ba yayin ziyarar Mahama
Saif al-Islam Gaddafi: An kashe ɗan marigayi shugaban Libya Muammar Gaddafi
Afirka na fuskantar tarnaƙin bashin dala biliyan 90 a 2026, in ji S&P
Yadda Biteye na Senegal ke amfani da ƙwallon ƙafa don samun waraka ga ƙwaƙwalwa
Sojojin Rasha sun taimaka wajen daƙile hari a filin jirgin saman Nijar: Moscow
'Yanbindiga sun kashe sojojin Libya uku a kusa da kan iyakar Nijar
Sudan ta sake buɗe filin jiragen sama na Khartoum bayan yaƙin kusan shekaru uku
Nijar: Ƙungiyar Daesh ta ɗauki nauyin harin da aka kai sansanin sojin sama na Yamai
Fiye da mutum 200 sun rasu bayan ruftawar wurin haƙar coltan a Jamhuriyar Kongo
Ƙungiyar Tarayyar Afirka ta sha alwashin goyon bayan Nijar bayan kai hari a filin jirgin saman Yamai