| Hausa
AFIRKA
2 MINTI KARATU
'Yan bindiga sun kashe malamin jami'a a Katsina, sun sace 'ya'yansa
Rahotanni sun ce 'yan bindigar sun afka gidan malamin da tsakar dare inda suka kashe shi suka kuma sace yaransa biyu.
'Yan bindiga sun kashe malamin jami'a a Katsina, sun sace 'ya'yansa
Kashe malamin na zuwa ne mako guda bayan kashe mataimakin Shugaban Jami’ar Usman Danfodio da ke Sokoto Farfesa Yusuf Saidu. / Hoto: Others / Others
2 Yuli 2024

Rahotanni daga Jihar Katsina a arewacin Nijeriya na cewa ‘yan bindiga sun kashe wani malamin Jami’ar Tarayya ta Dutsinma.

Rahotanni sun ce lamarin ya faru ne a ranar Talata da tsakar dare da misalin ƙarfe 1:30 inda ‘yan bindigar suka afka gidan Dakta Tiri Gyan da ke Yarima Quarters a Ƙaramar Hukumar Dutsinma.

Mai magana da yawun ‘yan sandan Nijeriya reshen Katsina Abubakar Sadiq ya tabbatar wa kafar watsa labarai ta Channels a Nijeriyar da kisan malamin.

Waɗanda suka shaida lamarin sun bayyana cewa ‘yan bindigar sun afka gidan malamin jami’ar da makamai daban-daban inda suka yi ta harbi domin tsorata mazauna rukunin gidajen.

Sun kuma bayyana cewa ɓarayin sun sace yara biyu na Dakta Gyan a lokacin da suka kai harin.

Kashe malamin na zuwa ne mako guda bayan kashe mataimakin Shugaban Jami’ar Usman Danfodio da ke Sokoto Farfesa Yusuf Saidu.

An kashe shi a lokacin da yake hanyarsa ta zuwa Kaduna daga Sokoto.

MAJIYA:TRT Afrika da abokan hulda